| hausa
TURKIYYA
1 minti karatu
Jami'an Turkiyya da Syria sun gudanar da tattaunawa kan tsaro a Ankara
Ministocin harkokin waje da na tsaro da shugabannin leƙen asiri na Turkiyya da Syria sun yi ganawa ta musamman inda suka tattauna kan tsaro tsakanin ƙasashen biyu da ci gaban da aka samu a ‘yan kwanakin nan a yankin.
Jami'an Turkiyya da Syria sun gudanar da tattaunawa kan tsaro a Ankara
Taron ya mayar da hankali kan haɗin gwiwar tsaro tsakanin Turkiyya da Syria, da kuma ci gaban da aka samu kwanan nan.
12 Oktoba 2025

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hakan Fidan da Ministan Tsaro Yasar Guler, da Shugaban Hukumar Leƙen Asiri Ibrahim Kalin sun gana a ranar Lahadi a Ankara tare da takwarorinsu na Syria don tattaunawa a matakin ƙoli.

A cewar majiyoyin diflomasiyya, Fidan, Guler, da Kalin sun tattaunawa tare da Ministan Harkokin Wajen Syria Asaad Hassan al Shaibani da Ministan Tsaro Murhaf Abu Qasra, da Shugaban Hukumar Leken Asiri Hussein Salameh a ranar Lahadi.

Taron ya mayar da hankali kan haɗin gwiwar tsaro tsakanin Turkiyya da Syria, da kuma ci gaban da aka samu kwanan nan.

A ranar Asabar, Ministan Tsaron Syria Murhaf Abu Qasra ya gana da Shugaban Hukumar Masana'antar Tsaro ta Turkiyya Haluk Gorgun tare da tawagarsa a birnin Dimashƙu.

A cewar wata sanarwa daga Ma'aikatar Tsaron Syria da aka wallafa ta tashar Telegram dinta, ɓangarorin biyu sun tattauna kan batutuwa daban-daban na moriyar juna kuma sun bincika hanyoyin ƙarfafa haɗin gwiwa a fannin tsaro.

Rumbun Labarai
Turkiyya na jimamin tunawa da rasuwar Ataturk shekara 87 da suka wuce
Nasarar da aka samu a yankin Karabakh na Azerbaijan babbar nasara ce ga yankin Caucasus: Erdogan
Turkiyya ta yi umarnin kama Firaministan Isra'ila Netanyahu da wasu mutane kan kisan kiyashi a Gaza
Turkish Airlines ya sayi hannun jari na dala miliyan 355 a kamfanin Air Europa na Spain
Erdogan ya yi Allah wadai da kashe fararen-hula a birnin Al Fasher na Sudan
Za a gudanar da tattaunawa a Istanbul kan yarjejeniyar tsagaita wutar Gaza da matsalolin jinƙai
Tsarin duniya na yanzu ya fi ba da fifiko kan iko fiye da adalci: Babban Daraktan TRT Sobaci
Hamas ba ta da nukiliya, amma Isra'ila na da su: Erdogan ya nemi Berlin ta ɗauki mataki kan Tel Aviv
Ana shirin fara taron TRT World Forum karo na 9 a Istanbul
Cikin hotuna: Yadda aka yi bukukuwa a duk faɗin kasa na cikar Ranar Jamhuriya ta Turkiyya ta 102
Turkiyya ta yi kira a tsagaita wuta nan-take a yaƙin da ake yi a birnin Al Fasher, Sudan
Turkiyya za ta mika wa dakarunta tankar yaki ta Altay da aka samar da yawa a karon farko
Kungiyar ta'addanci ta PKK ta sanar da janyewa baki ɗaya daga Turkiyya
Babu wani lissafin siyasa ko na tsaro da zai yiwu a duniya ba tare da Turkiyya ba: Erdogan
Rumfar Karfe: Fasahar Turkiyya ta cikin gida mai aiki da Ƙirƙirarriyar Basira a sabon zamanin tsaro
Shugaba Erdogan ya shirya ziyartar yankin Gulf don haɓaka alaƙar tattalin arziki da ƙawance
Turkiyya ta yi maraba da yarjejeniyar tsagaita wutar Afghanistan da Pakistan
An Fara Taron Yaki da Shara na ‘Zero Waste’ a Istanbul karkashin jagorancin Emine Erdogan
Matar Shugaban Turkiyya Emine Erdogan ta yi kira a bunkasa shigar mata cikin harkokin duniya
Cinikayya tsakanin Turkiyya da Afirka ta wuce $37b ana sa ran ta kai $40b a 2025: Minista