| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Iran na iya janyewa daga yarjejeniyar tsagaita wuta idan Isra'ila ta cigaba da yaƙar Lebanon: Rahoto
Iran na duba yarjejeniyar bayan zargin cewa Isra'ila ta maimaita keta haddi, ciki har da hare-haren masu yawa a Lebanon, cewar kafofin yaɗa labarai na yanki.
Iran na iya janyewa daga yarjejeniyar tsagaita wuta idan Isra'ila ta cigaba da yaƙar Lebanon: Rahoto
Masu ceto suna tsaye cikin tarkace a wurin harin Isra'ila a birnin Tyre, Lebanon, ranar 8 ga Afrilu, 2026. / Reuters

Iran za ta janye daga yarjejeniyar tsagaita wuta da Amurka idan Isra’ila ta ci gaba da take ta, ta hanyar kai hare-hare kan Lebanon, in ji wata majiya mai tushe a hira da Tasnim News Agency, wata kafar labarai da ke kusa da gwamnatin Iran.

Majiya ta faɗa a ranar Laraba cewa, Iran za ta janye daga yarjejeniyar idan keta haddin tsagaita wuta na gwamnatin Zionist ta ci gaba da kai hare-hare kan Lebanon.”

Majiyar ta ƙara da cewa Tehran na nazarin halin da ake ciki saboda abin da ta bayyana a matsayin “ci gaba da keta dokokin tsagaita wuta” da aka danganta da hare-hare kan Lebanon.

A cewar majiyar, Amurka ta amince da dakatar da faɗa a dukkan fuskoki, ciki har da waɗanda suka shafi kai hari kan 'mujahidan Islama' na Lebanon, a ƙarƙashin wani shiri na tsagaita wuta na makonni biyu da aka gabatar.

Masu AlakaTRT Afrika - Sharuɗɗa 10 na zaman lafiya da Amurka ta amince da su a yarjejeniyar tsagaita wuta da Iran

Duk da haka, Isra’ila ta aikata abin da majiyar ta bayyana a matsayin “bayanannen keta dokokin tsagaita wuta” tun daga daren Laraba, ta hanyar ƙaddamar da hare-haren da ta ce sun kasance masu muni kan Lebanon.

Rundunar sojin Isra’ila ta ce, ta kai hari kan fiye da wurare 100 cikin mintuna 10 a faɗin yankuna daban-daban a Beirut, da Kwarin Beqaa, da kudancin Lebanon, a cikin abin da ta bayyana a matsayin harin haɗin gwiwa “mafi girma” tun farkon farmakin da ke gudana a Lebanon.

Isra’ila ta ƙaddamar da hare-haren sama da kuma farmakin ƙasa a kudancin Lebanon tun bayan harin ƙetare da Hezbollah ta kai a ranar 2 ga Maris, duk da cewa an kafa tsagaita wuta a watan Nuwamban 2024.

Hukumomin Lebanon sun ce aƙalla mutane 1,530 ne suka mutu, kuma 4,812 suka ji rauni a hare-haren Isra’ila.

Rumbun Labarai
An jikkata sojojin Isra’ila takwas yayin kutse a Lebanon duk da yarjejeniyar tsagaita wuta
Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta riƙa kai hare-hare Iran a asirce a yaƙin Amurka da Isra'ila: rahoto
Rusassun cocina, alamomin Kiristanci da salon hare-haren Isra’ila da ke ci gaba a Lebanon
Trump ya kira martanin Iran ga shawarar zaman lafiya abin da 'ba za a lamunta ba kwata-kwata'
Iran ta mayar da martani ga masu shiga tsakani na Pakistan kan shawarar Amurka ta kawo ƙarshen yaƙi
Saudiyya ta musanta zargin bayar da izinin amfani da sararin samaniyarta don ayyukan soja
Iran ta harba makamai masu linzami ga sojin Amurka bayan hari kan tankar dakon manta
Darussa daga sabon tsarin tafiyar da duniya: Ba za a iya sayen tsaro ba, amma dole a gina shi
Trump ya dakatar da shirinsa na taimaka wa jiragen ruwa wucewa ta Mashigar Hormuz
Shugabannin duniya na matsa wa Iran lamba yayin da ake fargabar batun tsagaita wuta zai iya rushewa
Harin da Amurka ta kai Mashigar Hormuz ya kashe fararen-hula 5, a cewar Iran
Iran ta ce duk wani shirin Amurka kan mashigar Hormuz zai zama keta yarjejeniyar tsagaita wuta
Iran ta ba Amurka wata guda don janye toshe tashoshin ruwanta da kawo ƙarshen yaƙin Iran da Lebanon
Buɗaɗɗiyar maƙabartar Gaza: Gawawwaki 8,000 sun maƙale, yayin da aikin kwashe ɓaraguzai ya tsaya cak
Iran ta kunna na'urar tsaron sama yayin da Trump ke fuskantar wa'adin ikon shiga yaki daga Majalisa
Isra'ila na rasa goyon bayanta a tsakanin matasa 'yan  Amurka - Rahoto
Za a ci gaba da tattaunawa tsakanin Amurka da Iran ta waya – Trump
Trump ya ce bai kamata Iran ta samu makamin nukiliya ba a liyafar da aka shirya wa Sarki Charles III
Netanyahu ya bayyana a kotu don shari'ar cin hanci da rashawa a karon farko tun soma yaƙin Iran
Rikicin Gabas ta Tsakiya na koyar da darasi: Turkiyya ta zama kan gaba a zaɓin ƙasashen Afirka