| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Netanyahu ya kira taron gaggawa bayan Hezbollah ta kai hari na ban mamaki ga sojin Isra'ila
Sojojin Isra'ila sun bayyana cewa Hezbollah ta shammace su bayan ta sauya salon yaƙinta inda ta harba gomman rokoki a can cikin garuruwan da ke arewacin Isra'ila.
Netanyahu ya kira taron gaggawa bayan Hezbollah ta kai hari na ban mamaki ga sojin Isra'ila
Netanyahu ya gudanar da taron tsaro na gaggawa bayan harba rokoki ya girgiza arewacin Isra'ila / AP

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya kira taron tsaro na gaggawa tare da jami'ai don tantance halin da ake ciki a arewacin Isra'ila, bayan ƙaruwar rikici da Tel Aviv a kudancin Lebanon, in ji wani rahoto.

Gidan talabijin na Channel 13 na Isra’ila ya ruwaito cewa Netanyahu ya shirya wannan taron tsaro na gaggawa tare da Ministan Tsaro Israel Katz, Shugaban Ma'aikatan Sojoji Eyal Zamir da manyan hafsoshin rundunar a yankin arewa.

Rahoton ya ce "sojojin Isra'ila sun yi mamaki da girman harin roka da kuma yadda Hezbollah ta sauya salonta na yaƙi a martaninta ga faɗaɗa ayyukan rundunar ƙasa ta Isra'ila a kudancin Lebanon."

Rahoton ya bayyana cewa "an harba ɗaruruwan rokoki daga Lebanon inda suka nufi arewa a ranar Asabar, kuma a karon farko tun bayan da aka fara tsagaita wuta a ranar 17 Afrilu, waɗannan rokoki sun kai garuruwan Safed da Nahariya" a arewacin Isra'ila.

Ya lura cewa akwai "rudani kwarai da rashin iko a arewa," yana kara da cewa, "Gwamnati ba ta damu da wannan ba."

Barazanar jirage marasa matuƙa

A wani lamari na daban, Radiyon Sojan Isra'ila ta a ranar Asabar ta ruwaito cewa an kunna jiniya sau 1,099 a arewacin ƙasar tun daga farkon wannan tsagaita wuta mai rauni tsakanin Isra'ila da Hezbollah.

Hezbollah ta ce ta ƙaddamar da harin jiragen marasa matuƙa da suka nufi sojojin Isra'ila kusa da garuruwan ‘yan kama-wuri-zauna na Natua da kuma sansanin soja Galilee a arewacin Isra'ila.

A 'yan makonnin nan, jirage marasa matuƙa na Hezbollah sun ƙara jawo damuwa a Isra'ila, inda Netanyahu ya kira su "babbar barazana" saboda wahalar da ake sha wurin ganinsu.

Isra'ila ta ci gaba da kai hare-hare kan Lebanon duk da tsagaita wuta, wadda aka tsawaita da kwanaki 45 tun daga 17 Mayu, bayan tattaunawar da ba kai tsaye ba da Amurka ta shiga tsakani.

Hare-haren Isra'ila tun daga 2 ga Maris sun kashe fiye da mutane 3,371 a Lebanon, a cewar Ma'aikatar Lafiya ta Lebanon.