| Hausa
DUNIYA
2 minti karatu
Ministan Wajen Saudiyya da takwarorinsa na Iran, Oman da Qatar sun tattauna kan zaman lafiyar yanki
Ministocin sun tattauna ne kan yadda za a yayyafa ruwa kan wutar da ke ruruwa a yankin a daidai lokacin da ake tsoron harin Amurka kan Tehran.
Ministan Wajen Saudiyya da takwarorinsa na Iran, Oman da Qatar sun tattauna kan zaman lafiyar yanki
Ministan Harkokin Waje na Saudiyya Yarima Faisal bin Farhan ya halarci wani taro na tattaunawa na yanki a Amman, Jordan a ranar Litinin / AP
15 Janairu 2026

Ministan Harkokin Waje na Saudiyya, Yarima Faisal bin Farhan, ya yi tattaunawa da takwarorinsa na Iran, Oman da Qatar don tattaunawa kan yadda za a yayyafa ruwa kan wutar da ke ruruwa a yankin a daidai lokacin da ake tsoron harin Amurka kan Tehran.

A cewar wata sanarwa daga Ma’aikatar Harkokin Waje, a ranar Alhamis ta fitar, bin Farhan ya yi magana ta waya da Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araghchi don tattauna abubuwan da ke faruwa a yankin da hanyoyin da za a inganta tsaro da kwanciyar hankali.

Ministan Harkokin Wajen Saudiyya da takwaransa na Oman, Badr Albusaidi, sun kuma yi bita ta waya kan abubuwan da ke faruwa a yankin da kokarin hadin gwiwa da nufin samar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin yankin, in ji kamfanin dillancin labaran ƙasar SPA.

Bin Farhan da Firaministan Qatar kuma Ministan Harkokin Waje Sheikh Mohammed bin Abdulrahman Al Thani sun tattauna kan kokarin inganta tsaro da kwanciyar hankali a yankin, in ji SPA.

Trump ya sassauta magana kan Iran

Wannan kai ziyara ta diflomasiyya ta biyo bayan yadda Shugaban Amurka Donald Trump ya sassauta maganganu kan Iran a jawabin da ya yi a Fadar White House a ranar Laraba da dare.

Trump ya ce an sanar da shi cewa an dakatar da hukuncin kisa a Iran, amma ya yi gargaɗi cewa "idan wani abu makamancin haka ya faru, za mu ji baƙin ciki gaba ɗaya."

Tsoron yiwuwar harin Amurka kan Iran ya karu a cikin 'yan kwanakin da suka gabata, inda ake zanga-zangar adawa da gwamnati ƙasar tun karshen watan da ya gabata saboda tabarbarewar halin tattalin arziki a ƙasar.

A ranar Laraba, gidan rediyon gwamnati na Isra’ila ya ruwaito cewa nazarin Isra’ila ya nuna cewa Amurka na iya kai hari cikin Iran a cikin kwanakin da ke tafe.

Jami’an gwamnatin Iran sun zargi Amurka da Isra’ila da goyon bayan abin da suka bayyana a matsayin "hargitsi" da "ta'addanci" a tsakiyar zanga-zangar da ke gudana.

Hukumomin Iran ba su fitar da ainahin ƙididdigar wadanda suka mutu ko wadanda suka mutu da waɗanda aka tsare ba. Wata ƙungiyar kare hakkin ɗan’adam mai hedkwata a Amurka ta kiyasta cewa fiye da mutum 2,600 ne suka rasa rayukansu, ciki har da masu zanga-zanga da jami’an tsaro.

Rumbun Labarai
Saudiyya da Isra'ila za su Amurka don tattaunawa yayin da Trump ke tura jiragen yaƙi na ruwa Iran
WHO: Amurka ta fita daga Hukumar Lafiya ta Duniya bayan shekara 78
Masana kimiyya sun gano zanen shacin hannu 'mai shekara 67,800' a wani kogo a Indonesia
Amurka ta dakatar da ba da bizar masu ƙaura ga 'yan Nijeriya da wasu ƙasashe 74
Wani sanatan Amurka ya yi gargaɗi kan ƙaruwar ƙyamar Musulunci da ƙin jinin Larabawa
Trump ya saka harajin kashi 25 kan ƙasashen da ke kasuwanci da Iran
An katse intanet da wayoyin hannu a Iran
Matar shugaban Turkiyya ta gana da shugaban UNRWA kan shirin buɗe ofis a Ankara
Sanatocin Republican 5 sun bi sahun 'yan Democrat don neman sake duba ikon yaki na Trump a Venezuela
An kashe ɗansanda a kusa da Tehran yayin da zanga-zanga kan matsin rayuwa ta mamaye ƙasar Iran
Erdogan da Anwar na son ƙarfafa alaƙar Turkiyya da Malaysia tare da fifita fannin tsaro
Trump ya sanya hannu kan takardar neman cire Amurka daga ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa da na MDD
Shugaban Rundunar Sojin Iran ya yi barazanar mayar da martani ga Trump da Netanyahu
Abin da ya sa ya kamata Afirka ta damu kan samamen da Amurka ta kai Venezuela
An sayar da kifi mai nauyin kilogiram 240 a kan Naira biliyan 4.5 ($3.2m) a Japan
Me zai faru ga takunkuman da Amurka ta sanya wa Venezuela bayan ta ɗauke Maduro
Tarayyar Afirka ta nuna 'damuwa', Afirka ta Kudu ta nemi a yi taron MDD da gaggawa kan Venezuela
Trump ya gargaɗi Colombia, ya nufi Cuba bayan ya kama Maduro
Amurka ba za ta bari kowa ya ci gaba daga inda Maduro ya tsaya ba - Trump
Martanin duniya na karuwa kan hare-haren da Amurka ta kai wa Venezuela