| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Matatar Dangote ta ce tana da isasshen man jirgi da za ta iya wadatar da bukatun “duniya"
Matatar Mai ta Dangote a Nijeriya mai ƙarfin tace gangar mai 650,000 a kowace rana tana da isasshen man jirgin sama da za ta iya fitarwa zuwa kasuwannin duniya baki ɗaya, in ji Babban Daraktan kamfanin, David Bird, a ranar Talata.
Matatar Dangote ta ce tana da isasshen man jirgi da za ta iya wadatar da bukatun “duniya"
Matatar Dangote ta ce tana da isasshen man jirgi da za ta iya wadatar da bukatun “duniya" / Reuters

Matatar Mai ta Dangote a Nijeriya mai ƙarfin tace gangar mai 650,000 a kowace rana tana da isasshen man jirgin sama da za ta iya fitarwa zuwa kasuwannin duniya baki ɗaya, in ji Babban Daraktan kamfanin, David Bird, a ranar Talata.

Ya ce saboda bukatar mai a nahiyar Afirka ba ta kai ta sauran yankuna ba, kuma matatar na samun rarar da za ta iya fitarwa zuwa ƙasashen waje.

“Mun yi matuƙar godiya da yadda ake kallonmu a matsayin amintacceiyar mai samar da mai mai inganci kuma abin dogaro, wanda ke iya kai kayansa cikin farashi mai sauki zuwa ko ina a duniya,” in ji Bird yayin wani taro na S&P Global Energy Middle East Petroleum and Gas Conference a birnin London.

Ya kuma bayyana cewa man jirgin sama na daga cikin nau’o’in mai da rikicin Iran da kuma rufe Mashigar Hormuz suka fi shafa sosai a baya-bayan nan.

Shirye-shiryen faɗaɗa ƙarfin tace mai

Wannan dama ce ga matatun mai da ke wajen yankin Gulf, kamar Matatar Dangote, su shiga kasuwannin duniya wajen samar da mai.

Bird ya ce matatar tana aiki a cikakken ƙarfin da aka tsara mata a halin yanzu.

Ya kuma bayyana cewa ana shirin wani aikin faɗaɗa ƙarfin matatar da ya kira “ruthless replication” domin ninka yawan abin da take tacewa.

“Za mu ƙara ƙarfin tace gangar mai 700,000 a kowace rana nan da ƙarshen shekarar 2028,” in ji Bird, yana mai cewa an riga an sayo muhimman kayan aikin da ke ɗaukar dogon lokaci kafin su iso, kuma kamfanin na kan matakin bayar da kwangilolin gine-gine.

Ya ce kungiyar na iya kaiwa ga tace gangar mai miliyan 2.1 a kowace rana idan aka ƙara wata matatar a yankin Gabashin Afirka nan gaba, wanda zai sa ta zama babbar mai taka rawa a kasuwannin danyen mai da kuma man da aka tace.

Bird ya kuma ce Nijeriya ta sauya daga fuskantar ƙarancin mai zuwa cikakken wadatar mai tun bayan fara aiki da Matatar Dangote.

Rumbun Labarai
Tsayar da Obi ɗan takarar NDC ya sake share fagen fafatawar manyan 'yan takara uku a Nijeriya
NAHCON ta ba da umarnin bincike kan wani abinci da mahajjata suka ƙi ci kan 'rashin inganci'
Masu tayar da ƙayar baya 30,000 na rura wutar rashin tsaro a Nijeriya - Rahoton Amurka
'Yanbindiga sun yi garkuwa da mutum 10 tare da kona gidan wani sarki a jihar Kwara a Nijeriya
Sojojin Nijeriya sun kashe ‘yanta’adda 12 da ƙwato makamai a Borno
Wa zai fafata da Tinubu? Jam'iyyun siyasar Nijeriya na zaɓen fitar da 'yan takarar shugabancin ƙasar
Kotu ta soke jadawalin INEC game zabukan fitar da gwani da tsayar da 'yantakara na 2027
Tinubu ba shi da shirin sauya sunan Nijeriya ko soke shari'ar Musulunci a arewa – Fadar gwamnati
Hukumar Alhazan Nijeriya ta kammala jigilar maniyyatan ƙasar zuwa Saudiyya
Fitaccen Fasto a Nijeriya ya ba magoya bayan Arsenal haƙuri kan 'saƙon wahayin ƙarya' da ya isar
Wasu sun nemi na mutu saboda tallafin mai da canjin dala— Tinubu
NDLEA ta tarwatsa ƙungiyar masu hada miyagun ƙwayoyi ta Nijeriya da Mexico ta kama mutum 10
Sojojin Nijeriya 'bakwai ne' suka mutu a wani harin kwanton ɓauna na'yanta'adda a Jihar Sokoto
An kashe shugabannin Daesh 175 a arewa maso gabashin Nijeriya a farmakin haɗaka da Amurka
An sace yara da manya 46 a hare-haren makarantu a kudancin Nijeriya
Rundunar Sojin Amurka da ke aiki a Afirka ta ƙara kai sabbin hare-hare kan 'yanta'adda a Nijeriya
Babbar Kotun Tarayya a Abuja Nijeriya ta ba da belin Nasir El-Rufai kan naira miliyan 100
Nasarori da jayayya da mamaki sun karaɗe zaɓukan fid da gwani na Majalisar Wakilan APC a Nijeriya
Nijeriya ta tsananta sa ido bayan WHO ta ayyana dokar ta-baci kan Ebola da ta kashe mutum 88 a Congo
Rundunar 'yansandan Nijeriya ta tabbatar da kashe jami'anta 17 a harin ta'addanci a Jihar Yobe