| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Kotu ta soke jadawalin INEC game zabukan fitar da gwani da tsayar da 'yantakara na 2027
Alƙalin kotun, Maishari’a Mohammed Umar ya soke wa’adin ranar 10 ga watan Mayu da INEC ta gindaya, wani wa’adi da ke buƙatar dukkan jam’iyyuu siyasa su miƙa rijistar dukkan mambobinsu a matsayin sharaɗi na samun damar shiga manyan zaɓuka.
Kotu ta soke jadawalin INEC game zabukan fitar da gwani da tsayar da 'yantakara na 2027
Kotu ta soke jadawalin INEC game zaben da fid da gwani, da tsayar da 'yantakara na 2027 / Reuters

Yayin da manyan zaɓukan shekarar 2027 ke ƙaratowa, jam’iyyun siyasa sun sami sauƙi bayan wata kotun tarayyar Nijeriya a Abuja ta soke jadawalin da hukumar zaɓe INEC ta fitar na gudanar da zaɓukan fid da gwani da tsayar da ‘yantakara.

A hukuncin da ya yanke, alƙalin kotun, Mai shari’a Mohammed Umar, ya soke wa’adin ranar 10 ga watan Mayu da INEC ta gindaya, wa’adin da ke buƙatar dukkan jam’iyyu su miƙa rijistar dukkan mambobinsu a matsayin sharaɗi na samun damar shiga zaɓuka.

Jaridar Vanguard ta ambato wani tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa, Gbenga Hashim yana cewa hukuncin kotun da ya soke wasu ɓangarori daga cikin jadawalin hukumar Zaɓe INEC na zaɓen 2027 ya gaskata matsayarsa daɗaɗɗiya cewa, hukumar zaɓen ta zarce wuce gona da iri a ƙarƙashin dokar zaɓe ta shekarar 2026.

Mai shari’a Umar ya ce wa’adin da hukumar ta sanya wa jam’iyyun siyasa na gudanar da zaɓukan fid da gwani kuma su miƙa, da janye ko kuma maye gurbin sunaye da bayanan ‘yantakara domin manyan zaɓukan “bai dace da tanade-tanaden dokar zaɓe ta shekarar 2026 ba.”

Hukuncin ya biyo bayan wata ƙara da jam’iyyar YP ta shigar, inda ta nemi a tilasta wa INEC ta yi biyayya ga wa’adin kwanaki 120 na miƙa rijistar ‘yanjam’iyya da bayanan ‘yan takara gabannin zaɓe, bisa dokar zaɓen 2026.

Mai shigar da ƙarar ya nemi kotun ta ayyana cewa idan aka yi la’akari da tanade-tanaden sashi na 29, 82 da sashi na 84(1) na dokar zaɓen shekarar 2026, ikon INEC na karɓar sanarwar zaɓukan fid da gwani da bayanan ‘yan takara da kuma nauyin da ya rataya a kanta na halarta da sa ido kan zaɓukan fid da gwani bai kai ga saka rana ko kuma jadawali na zaɓukan fid da gwani cikin jam’iyyu domin tsayar da ‘yan takara a zaɓukan shekarar 2027 ba.

Maishari’a Umar ya kuma yanke hukuncin cewa a tanade-tanaden sashi na 32 na dokar zaɓe ta shekarar 2026, INEC ba ta da ikon wallafa sunayen ‘yantakara na ƙarshe na zaɓukan 2027 kafin aƙalla kwanaki 60 gabannin zaɓen kamar yadda doka ta tanada.

Rumbun Labarai
Wasu sun nemi na mutu saboda tallafin mai da canjin dala— Tinubu
NDLEA ta tarwatsa ƙungiyar masu hada miyagun ƙwayoyi ta Nijeriya da Mexico ta kama mutum 10
Sojojin Nijeriya 'bakwai ne' suka mutu a wani harin kwanton ɓauna na'yanta'adda a Jihar Sokoto
An kashe shugabannin Daesh 175 a arewa maso gabashin Nijeriya a farmakin haɗaka da Amurka
An sace yara da manya 46 a hare-haren makarantu a kudancin Nijeriya
Rundunar Sojin Amurka da ke aiki a Afirka ta ƙara kai sabbin hare-hare kan 'yanta'adda a Nijeriya
Babbar Kotun Tarayya a Abuja Nijeriya ta ba da belin Nasir El-Rufai kan naira miliyan 100
Nasarori da jayayya da mamaki sun karaɗe zaɓukan fid da gwani na Majalisar Wakilan APC a Nijeriya
Nijeriya ta tsananta sa ido bayan WHO ta ayyana dokar ta-baci kan Ebola da ta kashe mutum 88 a Congo
Rundunar 'yansandan Nijeriya ta tabbatar da kashe jami'anta 17 a harin ta'addanci a Jihar Yobe
'Yanbindiga a Nijeriya sun sace ɗaliban da ba a san adadinsu ba a Jihar Borno
Dakarun Amurka da na Nijeriya sun kashe mataimakin shugaban Daesh, Abu-Bilal al-Minuki: Trump
An sallami 'yansandan Nijeriya biyar kan zargin fashi da makami a Jihar Ribas
Tinubu ya yi gargaɗi kan siyasar ‘a-mutu-ko-a-yi-rai’ a zaɓukan fid da gwani na Jam'iyyar APC
Nijeriya ta buƙaci shiga Hukumar Makamashi ta Duniya a IEA a matsayin memba
'Yanta'addan Lakurawa sun kashe jami'an hukumar kwastam biyu a Jihar Kebbi ta Nijeriya
Rundunar sojin Nijeriya ta ce babu shaida ta kashe fararen-hula a harin sama a kasuwa a Zamfara
Nijeriya na tattaunawa da Bankin Duniya kan sabon bashin $1.25bn: rahoto
Shugaba Tinubu na Nijeriya na halartar taron Afirka da Faransa a Kenya
Rundunar Sojin Nijeriya ta musanta kashe fararen-hula a harin sama a jihar Neja