| hausa
NIJERIYA
1 minti karatu
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir
Wannan ne karon farko da gwamnatin Kano za ta gabatar da kasafin kuɗi da ya haura naira tiriliyan ɗaya, a cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan na Kano Sanusi Bature ya fitar ranar Juma’a.
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir
A mako mai zuwa Gwamna Abba zai gabatar da kudirin kasafin a gaban majalisar dokokin jihar.
14 Nuwamba 2025

Gwaman Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ce zai gabatar da kasafin kuɗin shekara mai zuwa ta 2026 da ya haura naira tirilyan daya.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ranar Juma’a ta ce wannan ne karon farko da gwamnatin Kano za ta gabatar da kasafin kuɗi da ya haura naira tiriliyan daya.

Sanarwar ta ce gwamnan ya bayyana haka ne yayin da ya ke buɗe Taron Majalisar Zartarwa na Musamman don tattaunawa kan ƙudirin kasafin kuɗin na badi, wanda za a mika shi ga majalisar dokokin jihar a makon gobe.

Gwamna Abba ya ce kasafin kuɗin zai mayar da hankali kan ci gaba da ayyukan da ake yi yanzu, da sabunta birane da bunƙasa harkokin tattalin arziki a faɗin jihar.

Sauran ɓangarorin da za a bai wa muhimmanci a cewar sanarwar sun haɗa da bunƙasa gidaje da aikin gona da ilimi da tallafa wa matsakaita da kananan masana’antu, da nufin haaɓka tattalin arzikin jihar.

Ya ƙara da cewa girman kasafin kuɗin yana da dangantaka da bunƙasa hanyoyin samun kuɗaɗen shiga, da kuma toshe hanyoyin da kueɗaɗn gwamnati ke zurarewa.

Rumbun Labarai
Jerin lokutan da aka shafe ana shari'ar Nnamdi Kanu, jagoran 'yan a-waren Biafra a Nijeriya
Yadda ta kaya a zaman 'yan majalisar Amurka kan zargin yi wa Kirisotci kisan kiyashi a Nijeriya
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da 'yan ta'adda suka kashe a Borno
Majalisar Dokokin Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi  a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Rikicin PDP: Ɓangaren Wike ya yi watsi da kora yayin da jihohi huɗu ke ƙalubalantar Makinde
‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?