| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Rundunar sojin Chadi ta ce an kashe jami'anta 23 a wani harin Boko Haram
Bayan harin Oktoban 2024, Shugaba Deby ya ƙaddamar da harin fansa inda ya sha alwashin jan ragama "shi da kansa" don kai hari tsawon makonni biyu.
Rundunar sojin Chadi ta ce an kashe jami'anta 23 a wani harin Boko Haram
Tafkin Chadi ya zama wata matattara ta mayaƙa 'yan-ta'adda / Reuters

Wani hari da aka kai cikin dare da ake zargin 'yanta'addar Boko Haram ne suka kai a wani sansanin sojojin Chadi ya halaka aƙalla mutum 24, a cewar wani jami’in soji ranar Talata.

Jami’in sojin yankin ya faɗa wa kamfanin dillacin labaria na AFP cewa harin ya faru ne a sansanin soji na Barka Tolorom da ke gaɓar Tafkin Chadi, mai iyaka da Kamaru, Nijar, da Nijeriya.

Majiyar ta gaya wa AFP cewa farmakin ya faru ne a daren Litinin, kuma ya "bar mutum 25 a mace, da kuma mutum 46 da raunuka a ɓangaren sojin Chadi".

Jami’in da aka zanta da shi ya ambaci "kisan mutum 24 da kuma tarin masu raunuka."
Duka majiyoyin sun ɗora alhakin harin kan Boko Haram, inda jami’in ya jaddada cewa "lamura sun lafa."

Shugaban Chadi, Mahamat Idriss Deby Itno ya wallafa a Facebook ranar Talata cewa, "Ta kuma faruwa, ƙungiyar ta’adda ta Boko Haram ta ƙaddamar da hari a daren jiya kan sansanin sojinmu a Barka Tolorom".

Ya sha alwashin cewa, "Za mu ci gaba da yaƙi da jaddada aniya har sai wannan barazanar an kau da ita gabaɗaya”. Sannan shugaban ya miƙa saƙon ta’azaiyya ga iyalan waɗanda abin ya shafa.

Ƙaruwar hare-hare

Ana samun ƙaruwar farmaki kan sojoji daga Boko Haram a yankin Tafkin Chadi, inda wani hari na Oktoban 2024 ya halaka mutum 40 cikin rukunin sojin Chadi.

A watannin baya-bayan nan an samu ƙarin ƙaimi a hare-haren rassan ƙungiyar ta’adda ta JAS, har da satar mutane da hari kan tawagogin soji, musamman kan tsibirai da ke gaɓar tafkin da ke yankin Nijar.

Bayan wancan harin na Oktoban 2024, Shugaba Deby ya ƙaddamar da harin fansa inda ya sha alwashin jan ragama "shi da kansa" don kai hari tsawon makonni biyu.

Lokacin da harin fansar ya zo ƙarshe a Fabrairun 2025, rundunar sojin Chadi ta ce babu sauran "maɓoyar [Boko Haram] a iyakokin Chadi."

Tsibiran da ke cikin Tafkin Chadi ya zama wata mafaka ta mayaƙan Boko Haram da sauran gungun ‘yan-ta’adda da suka addabi yankin, ciki har da wani ɓurɓushin Boko Haram na ISWAP.