| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Rundunar Sojin Nijeriya ta ƙaryata wani rahoto na bogi da ke yawo a kafafen sada zumunta wanda ya yi zargin cewa an sace wani Birgediya Janar a Borno.
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Shugaban Sojojin Ƙasa na Nijeriya, Laftanar Janar Waidi Shaibu ya yaba da jaruntaka, juriya, da sadaukarwar sojojin.
15 Nuwamba 2025

Sojojin haɗaka na Brigade ta 25 da ke sintiri domin kare al’ummomi a yankin Wajiroko da ke Azir–Multe, cikin Karamar Hukumar Damboa a Borno, sun fuskanci kwanton-ɓauna mai tsanani daga ‘yan ta’adda a ranar Juma’a yayin da suke komawa bayan nasarar da suka samu a kusa da dajin Sambisa.

Rundunar, wadda Brigediya Janar M. Uba, Kwamandan Brigade ta 25, ya jagoranta, ta haɗa da sojoji da kuma jami’an kare farar-hula na Civilian Joint Task Force (CJTF), kamar yadda rundunar sojin Nijeriya ta bayyana a wata sanarwa da ta fitar a ranar Asabar.

Duk da irin ƙarfi da ƙwaƙƙwaran harbin da suka sha, sojojin sun mayar da martani da iya ƙarfinsu, suka daƙile kwanton-ɓaunar, sannan suka tilasta wa ‘yan ta’addan tserewa cikin ruɗani tare da barin shirin da suka zo da shi.

Sai dai rundunar ta tabbatar da cewa sojoji biyu da kuma mambobin CJTF biyu sun rasa rayukansu a yayin arangamar. Rundunar Sojan ta bayyana su a matsayin “jarumai masu kishin ƙasa,” tare da miƙa ta’aziyya ga iyalai da abokan aikinsu kan wannan sadaukarwa ta ƙarshe da suka yi wa Nijeriya.

Haka kuma rundunar sojin ƙasar ta kuma ƙaryata wani rahoto na bogi da ke yawo a kafafen sada zumunta da ya yi zargin cewa an sace Birgediya Janar ɗin da ke jagorantar rundunar.

Rundunar sojin ta buƙaci jama’a da su yi watsi da wannan labari na ƙarya, tare da tabbatar da cewa kwamandan yana cikin ƙoshin lafiya kuma yana kan aikinsa yadda ya kamata.

Haka kuma Shugaban Sojojin Ƙasa na Nijeriya, Laftanar Janar Waidi Shaibu ya yaba da jaruntaka, juriya, da sadaukarwar sojojin.

 

Rumbun Labarai
Jerin lokutan da aka shafe ana shari'ar Nnamdi Kanu, jagoran 'yan a-waren Biafra a Nijeriya
Yadda ta kaya a zaman 'yan majalisar Amurka kan zargin yi wa Kirisotci kisan kiyashi a Nijeriya
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da 'yan ta'adda suka kashe a Borno
Majalisar Dokokin Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi  a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Rikicin PDP: Ɓangaren Wike ya yi watsi da kora yayin da jihohi huɗu ke ƙalubalantar Makinde
‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir
Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?