AFIRKA
2 minti karatu
ICC ta tuhumi shugaban ‘yan bindiga na Sudan Ali Kushayb da laifukan keta hakkin bil’adama
Tuhumar ce hukuncin ICC na farko da ya shafi rikicin Darfur kuma ana sa rai zai zama misalin yin adalci a ɗaya daga cikin rikice-rikicen jinƙai mafiya daɗewa a Afirka.
ICC ta tuhumi shugaban ‘yan bindiga na Sudan Ali Kushayb da laifukan keta hakkin bil’adama
Ali Muhammad Ali Abd-Al-Rahman ya halarci zaman kotun ta ta ICC a yayin da ma shari'a ya bayyana hukuncin da aka yanke amsa kan laifukan yaki.
7 Oktoba 2025

Kotun hukunta manyan laifuka ta ƙasa da ƙasa a ranar Litinin ta samu wani babban jagoran mayakan sa-kai na Sudan da laifi bayan an kai ƙararsa kan zargin aikata laifukan yaƙi da cin zarafin bil’adama a lokacin kai munanan hare-hare a yankin Darfur.

An tuhumi Ali Muhammad Ali Abd-Al-Rahman, wanda aka fi sani da nom de guerre Ali Kushayb da laifuka da dama da suka haɗa da fyaɗe, kisa da azabtarwa da aka yi a tsakanin watan Agustan 2003 zuwa Afrilun 2004.

Binciken da kotun ta ICC ta yi ya gano cewa Kushayb ya jagoranci kai hare-hare kan fararen-hula a lokacin yaƙin Darfur, wanda ya yi sanadin mutuwar dubban ɗaruruwan mutane tare da raba miliyoyi da matsugunansu. An mayar da shi hannun kotun ICC a ranar 9 ga watan Yunin 2020 bayan ya miƙa kansa a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, kuma ya a karon farko ya bayyana a gaban kotu a ranar 15 ga Yunin 2020.

Bayan sauraren ƙarar a watan Mayun 2021, kotun ta tabbatar da laifuka 31 na laifukan yaƙi da cin zarafin bil’adama tare da gurfanar da Kushayb a gabanta.

An fara zaman shari'ar a hukumance a ranar 5 ga Afrilun 2022, tare da mutane 56 da za su bayar da shaida yayin shari'ar.

Wakilan waɗanda abin ya shafa su ma sun gabatar da ra'ayoyinsu, kuma masu kariya sun kira shaidu 18 kafin a saurari ƙarar a watan Disamban 2024.

Tuhumar ce hukuncin ICC na farko da ya shafi rikicin Darfur kuma ana sa rai zai zama misalin yin adalci a ɗaya daga cikin rikice-rikicen jinƙai mafiya daɗewa a Afirka.

Rumbun Labarai
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya
Dubban mutane sun tsere daga North Kordofan yayin da RSF ta zafafa kai hari a yankin Darfur na Sudan
Fararen-hula 177,000 sun maƙale a Al Fasher na Sudan, yayin da RSF ke ci gaba da kisa - Likitoci