| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Sojojin Nijeriya sun kashe 'yanta'adda da dama a Borno da Adamawa
Sojojin na Nijeriya sun samu nasarar ƙwato makamai da harsasai da bama-bamai daga hannun 'yanta'addan.
Sojojin Nijeriya sun kashe 'yanta'adda da dama a Borno da Adamawa
Sojojin sun jawo wa ‘yanta’addan waɗanda ke tserewa asara babba a lokacin da suke kai musu farmaki. / Nigerian army
17 Janairu 2026

A wata gagarumar nasara a yaƙi da ta’addanci, sojojin Rundunar Haɗin Gwiwa na Operation Hadin Kai sun kashe ’yanta’adda da dama a Jihohin Adamawa da Borno da ke arewa maso gabashing Nijeriya.

Mukaddashin Jami’in Watsa Labarai na rundunar, Laftanar Solomon Atokolo, ya ce nasarar ta biyo bayan dakile wasu hare-haren ’yanta’adda da aka shirya a sassa daban-daban na jihohin Arewa Maso Gabas.

Atokolo ya ce sojojin sun jawo wa ‘yanta’addan waɗanda ke tserewa asara babba a lokacin da suke kai musu farmaki.

 “A safiyar ranar 16 ga Janairun 2026, ’yanta’adda sun yi yunkurin kwace sansanin sintiri a Sabon Gari da ke Karamar Hukumar Madagali a Jihar Adamawa, karkashin Sashe na 4 na OPHK. Sojojin da ke cikin shiri sun gaggauta tunkarar maharan, tare da samun tallafi daga dakarun da suka fito daga Gulak da kuma Rundunar Gaggawa ta Bataliya,” in ji shi a cikin wata sanarwa.

“An yi nasarar fatattakar ’yanta’addan ba tare da asarar rai ko kayan aiki daga bangaren sojojinmu ba, lamarin da ya tilasta musu barin harin,” in ji wani bangare na sanarwar.

Masu AlakaTRT Afrika - Amurka ta aika kayayyakin soji ga Nijeriya bayan ƙaddamar da ayyukan tsaro na haɗin gwiwa

A cewarsa, daga bisani an tsaftace yankin gaba ɗaya daga ‘yanta’adda tare da bincika shi domin gano nakiyoyi da tarko na bama-bamai, don tabbatar da tsaron fararen-hula da sojoji.

Haka kuma duk a rana ɗaya, ’yanta’adda sun kai wani babban hari daga fannoni da dama kan sansanin soji na FOB da ke Azir a Jihar Borno.

Maharan sun yi ƙoƙarin karya wani ɓangare na garkuwar tsaro, amma jaruman sojoji sun tarbe su inda suka buɗe musu wuta, tare da samun goyon bayan Sashen Sojojin Sama da sauran jiragen saman Rundunar Sojin Njeriya, lamarin da ya tilasta wa ’yanta’addan janyewa.

A yayin artabun, harbin makaman roka (RPG) da ’yanta’addan suka yi ya shafi motocin ɗaukar sojoji da ɗakin kula da kyamarorin CCTV, inda aka samu gobara a wani ɓangare, amma duk da haka sojojin sun ci gaba da rike cikakken iko da yanayin.

An kwato makamai da alburusai da dama daga hannun ’yanta’addan, ciki har bama-baman mortar da abubuwan fashewa da aka ƙera a gida, harsasan manyan bindigogi, da ɗaruruwan harsasan 7.62mm na NATO.

Rumbun Labarai
Rundunar Sojin Nijeriya ta ce ta daƙile hare-haren 'yan ta'adda a jihar Borno
Nijeriya ta gargaɗi ‘yan ƙasar kan faɗawa tarkon masu ɗaukar ma’aikata su tura su wurin yaƙi
'Yanbindiga sun kashe aƙalla mutum 30 a Jihar Neja ta Nijeriya, sun ƙona ofishin 'yansanda
'Yanbindiga sun kashe DPO na 'yansandan Nijeriya a Jihar Katsina
'Rashin sake wa hukumomin gwamnatin Nijeriya kuɗaɗen kasafi koma-baya ne ga ci gaban ƙasa'
Za a yi zaben Shugaban Kasa a Nijeriya ranar 20 ga Fabrairun 2027, in ji INEC
Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Nijeriya ta kori ma'aikatanta 43 kan saɓa wa dokar aiki
Jami'an tsaro sun ƙwace fasfon Nasir El-Rufa'i bayan yunkurin kama shi ya ci tura a filin jirgi
Sojojin Nijeriya sun kashe 'yan Boko Haram 16 a Borno
CBN ya bai wa 'yan canji a Nijeriya damar sayen dala 150,000 a duk mako daga gwamnati
Amurka za ta tura sojojinta 200 Nijeriya
Sojojin Nijeriya sun kashe gomman 'yan-ta'adda, sun dawo da mutum 700 gida a arewa maso gabas
Me ya sa Kannywood ke fafutuka yayin da Nollywood ke samun tagomashi?
Shugaban Hukumar Alhazan Nijeriya Sheikh Abdullahi Saleh Pakistan ya ajiye aikinsa
Mutum fiye da 30 sun rasu sakamakon hatsarin mota a Jihar Kano
Nijeriya: 'Yanbindiga sun sace wani faston Katolika a Kaduna, sun kashe mutum uku
Nijeriya da Nijar sun ƙulla yarjejeniya kan jigilar kayayyaki da tsaron kan iyaka
Shugaba Tinubu na Nijeriya na shirin kai ziyarar aiki London a watan Maris
Jerin hare-hare sun yi sanadin mutuwar mutum 30 a Jihar Benue ta Nijeriya
Jami’an tsaron Nijeriya sun kwance wani bam da ‘yan ta’adda suka dasa a Zamfara