Jerin saƙonnin ta’aziyya suna ci gaba da shigowa daga faɗin Gabas Ta Tsakiya bayan wani jirgin helikwafta na soji da ya faɗi a cikin ruwan Qatar ya kashe mutum bakwai, ciki har da jami’ai daga dakarun Turkiyya da na Qatar da kuma wani babban jami’in kamfanin tsaron Turkiyya.
Ma’aikatun harkokin waje daga ƙasashen Saudiyya da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa da Bahrain da Kuwait da Iraki da Jordan da kuma Syria sun fitar da sanarwa suna masu bayyana tausayi da haɗin kansu ga ƙasashen biyu bayan aukuwar lamarin.
Ma’aikatar tsaron ƙasa ta Turkiyya ta ce jami’in sojin Turkiyya ɗaya da ma’aikatan fasaha biyu daga kamfanin ASELSAN na daga cikin waɗanda suka rasa rayukansu a lamarin.

Helikwaftan, na rundunar sojin Qatar, yana aiki ne a wani ɓangare na horaswa a ƙarƙashin runduna ta haɗin gwiwa ta Qatar da Turkiyya a lokacin da ta faɗa cikin teku da yammacin ranar Juma’a.
Binciken farko ya ce lamarin ya faru ne sakamakon matsalar na’ura, duk da cewa hukumomin Qatar sun ƙaddamar da cikakken bincike domin tabbatar da ainihin abin da ya janyo hatsarin.
Bala’i cikin ƙaruwar tashe-tashen hankula
Hatsarin jirgin na zuwa ne a wani lokaci na ƙaruwar rashin kwanciyar hankali na yankin bayan hare-haren da Amurka da Isra’ila suka ƙaddamar kan Iran da kuma ramuwar gayyar Tehran ta hare-haren jirage marasa matuƙa da na makamai masu linzami kan Isra’ila da ƙasashen Larabawa da ke gaɓar teku da ke da sansanonin sojin Amurka.
Yayin da alama ke nuna cewa tsautsayi ne ya haddasa lamarin, lokacin da lamarin ya faru ya nuna raunin yanayin tsaro a faɗin yankin, inda aka zafafa haɗin kan soji da ayyuka na haɗin gwiwa.
Yadda ake fitar da saƙonnin ta’aziyya sun nuna taimakekeniya na yanki yayin da Turkiyya da Qatar ke ji da rashin da kuma ƙalubalen tsaron da ke fuskantar Gabas Ta Tsakiya.















