| Hausa
WASANNI
3 minti karatu
Mohamed Salah ya sanya hannu kan kwantiragin shekaru biyu da Trabzonspor ta Turkiyya
Tauraron, ɗan ƙasar Masar zai riƙa karɓar albashin sama da dala miliyan 11.5 a kowace shekara da garaɓasar dala miliyan 8 a kowace kakar wasa.
Mohamed Salah ya sanya hannu kan kwantiragin shekaru biyu da Trabzonspor ta Turkiyya
Mohamed Salah ya koma ƙungiyar Trabzonspor ta Turkiyya bayan ya baro Liverpool

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Trabzonspor da ke Turkiyya ta tabbatar a ranar Alhamis cewa ta ɗauki Tauraron ƙwallon ƙafa na Masar Mohemed Salah kan wata yarjejeniya da a ƙarƙashinta zai riƙa ɗaukar dala miliyan 19.6 (€17 miliyan) a duk kakar wasanni.

Ɗanwasan na Masar, Salah ya rattaba hannu kan kwantiragin shekaru biyu ne bayan ya bar Liverpool ta Ingila a ƙarshen kakar bara.

Salah zai samu dala miliyan $19.6 duk kakar wasanni, wato albashin dala miliyan $11.5, da bonos ɗin dala miliyan $8. Haka nan, yana da damar samun garaɓasar gwargwadon ƙoƙarinsa, tare da kashi 20 daga amfani da sunansa.

Bayan kwashe shekaru tara a gasar Firimiya, mashahurin ɗanwasan mai shekaru 34 ya iso Turkiyya don buga babbar gasar ƙasar ta Super Lig, a matsayinsa na ɗanwasan da ba shi ƙungiya.

Tun a ranar Laraba ne Salah ya isa birnin Trabzon da ke bakin teku, kafin ya sanya hannu ranar Alhamis a sauyin sheƙar da ya ja hankalin masoya ƙwallo a duniya.

Salah ɗanwasan gaba ne mai farin jini, kuma ya samu nasarori da dama a ƙwallo, cikin har da lashe gasar Firimiya sau biyu, da gasar Zakarun Turai guda, da FA ɗaya, da Carabao ɗaya.

Batun tagomashi

Ɗanwasan ya samu gagarumar tarba daga dubban masoya Trabzonspor bayan saukar sa a filin jirgi sanye da rigar ƙungiyar, abin da ya ƙayatar da shi matuƙa.

Da yake jawabi yayin bikin tarbar tasa, Salah ya zayyana burukansa, yana cewa, "Ina matuƙar murna da kasancewata a wannan ƙayataccen waje. Ba na iya tuna na ga irin wannan taron kafin yau."

Gabanin barin Liverpool, Salah ya ci ƙwallaye 257 da tallafin ƙwallo 123 a wasanni 442 a duka gasannin da ya buga.

Sai dai a kakar ƙarshe da ya buga a Anfield tagomashinsa ya yi ƙasa, inda ƙwallo bakwai kacal ya ci a wasanni 27, wanda shi ne karo na farko da ya ci ƙwallaye ƙasa da 10 a kaka guda a Liverpool.

Sai dai Mohamed Salah ya ci gaba da kasancewa haziƙi abin alfahari a fagen ƙwallo, kasancewarsa kyaftin ɗin tawagar Masar a gasar Kofin Duniya ta 2026 da aka fitar da su a zagayen ‘yan-16.

Trabzonspor ce ta lashe kofin Turkish Cup a kakar da aka kammala, inda t ƙare lig da maki takwas a ƙasan Galatasaray da ta lashe kofin.

Rabon da Trabzonspor ta lashe gasar Super Lig tun kakar 2021-22. Don haka a bana suna fatan zuwan Salah ya ƙara musu armashi da tagomashi, inda za su nemi kofuna a gasanni ciki har da gasar Europa.

Rumbun Labarai
An manta da Raphinha da Pedri cikin 'yanwasa 30 da za su iya lashe kyautar Ballon d'Or
Barcelona ta miƙa ƙoƙon-bara wajen masu zuba jari don neman kuɗin gyaran filin wasa
Turkiyya ta kuma lashe kofin gasar volleyball ta mata ta nahiyar Turai
An yanke wa Tiger Woods hukuncin haramcin tukin mota tsawon shekaru 5 saboda tuki cikin maye
Muhimman batutuwa game da ritayar Messi daga tawagar Argentina
Sakon Lionel Messi na yin ritaya daga buga kwallo a matakin kasa-da-kasa
"Jikina ya fara sakwarkwacewa" in ji Djokovic, bayan an fitar da shi daga Gasar US Open ta bana
Shugaban Hukumar Ƙwallon Ƙafar Nijeriya Musa Gusau ya yi murabus
Ɗanwasan Kamaru Carlos Baleba ya koma Man Utd daga Brighton
Habasha ta shiga takarar ɗaukar nauyin gasar AFCON ta 2028
An sayar da ƙwallon da Maradona ya ci Ingila da hannu a kan $3.35M
Ɗan Nijeriya Semi Ajayi ya taimaka wajen yi wa Man Utd dukan wulaƙanci a farkon Gasar Firimiya
Cristiano Ronaldo ya fara kakarsa ta 25 da ƙwallonsa na 977 a tarihin wasansa
EFCC ta fara binciken Hukumar kwallon kafa ta Nijeriya, NFF
Jamal Musiala na Bayern Munich ya ce farfaɗiyar sandarewa ce ke damun sa
Patrick Vieira, tsohon ɗanwasan Arsenal ya zama sabon kocin tawagar Senegal
Kamaru ta lashe Kofin WAFCON a karon farko bayan ta doke Malawi
Lionel Messi ya ɓarar da fenareti na uku a jere yayin da aka lallasa kulob ɗinsa da ci 4-1
Ɗanwasan Sifaniya da ya ci Gasar Kofin Duniya Ferran Torres ya koma PSG daga Barcelona
Hukumomin ƙwallon ƙafa 6 na Larabawa, ciki har da Qatar da Morocco na goyon bayan Infantino na FIFA