Iran ta shaida wa shugaban MDD za ta mayar da martani 'mai ƙarfi' idan Amurka ta kai mata hari
Ofishin dindindin na Iran a Majalisar Dinkin Duniya a wata wasiƙa a ranar Alhamis ya bayyana cewa maganganun Shugaban Amurka Donald Trump game da Iran “na nuna wata barazana ta gaske ta farmakin soja”, ya kuma ƙara da cewa Iran ba ta so a yi yaƙi.
Iran ta shaida wa Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres cewa Tehran za ta ɗauki sansanonin da “dakarun maƙiya” suke amfani da su a yankunan a matsayin wuraren da za su iya kai wa hari idan an kai mata farmaki na soji.
Ofishin dindindin na Iran a Majalisar Dinkin Duniya a wata wasiƙa a ranar Alhamis ya bayyana cewa maganganun Shugaban Amurka Donald Trump game da Iran “na nuna wata barazana ta gaske ta farmakin soja”, ya kuma ƙara da cewa Iran ba ta so a yi yaƙi.
Wasiƙar ta ce Iran za ta mayar da martani “cikin ƙarfi” idan aka kai mata farmakin soja.
Martanin Iran ya biyo bayan yadda Trump ya yi gargaɗi cewa Iran dole ta cim ma “matsaya mai ma'ana” a tattaunawar da ake yi da Washington cikin kwanaki 10 masu zuwa idan ba haka ba “abubuwa marasa kyau za su iya faruwa”, a yayin da ya tura jiragen ruwa na yaki da jiragen sama na yaƙi da sauran kayan yaƙi zuwa yankin.
"A shekaru da dama an nuna cewa bai kasance mai sauƙi a cim ma matsaya mai ma'ana da Iran ba. Dole mu cim ma matsaya mai ma'ana idan ba haka ba abubuwa masu muni za su faru," in ji Trump a taron buɗe Kwamitin Zaman Lafiya, shirin nasa na tabbatar da kwanciyar hankali a Gaza.
Ya yi gargaɗin cewa Washington “na iya ɗaukar mataki mafi tsanani” idan ba a samu yarjejeniya ba, kamar yadda ya ƙara da cewa: “Za ku sani nan da watakila kwanaki 10 masu zuwa.”
Maganganun Trump sun zo ne ba da jimawa ba bayan Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya yi gargaɗinsa ga Iran yana cewa, “Idan su Ayatollah suka yi kuskure suka kai mana hari, za su sami martanin da ba za su taɓa zato ba”.
Samar da rundunonin soja don kai hari kan Iran
An fitar da waɗannan gargaɗin ne kwanaki bayan da Amurka da Iran suka gudanar da zagaye na biyu na tattaunawa a ƙarƙashin shiga tsakani na Oman, a wannan karon a Geneva, inda Amurka ke neman hana Iran samun bam din nukiliya — abin da Iran ke cewa ba ta nema — kuma Iran na neman saukaka takunkumin Amurka.
Amurka ta kasance tana ƙara karfafa sojojinta a kusa da Iran, ciki har da jiragen ruwa na yaƙi, jiragen sama na yaki, da jiragen zuba mai, tana gudanar da shirye-shirye don yiwuwar afka wa Iran.
Washington ta ba da umarni a tura wani jirgin ɗaukar jiragen yaki na biyu zuwa yankin, inda na farko, USS Abraham Lincoln da kusan jiragenta 80, suka kasance a matsayi kusan kilomita 700 daga gabar Iran a ranar Lahadi, kamar yadda hotunan tauraron ‘ɗanadam suka nuna.
Iran ta yi ƙoƙarin nuna ƙarfin na sojin, yayin da Rundunar “Juyin Juya Hali ta Iran” (IRGC) ta gudanar da atisaye na yaƙi a farkon makon nan a Tashar Hormuz.
Yan siyasar Iran sun sha yin barazanar toshe mashigin tekun, wata babbar hanyar duniya don jigilar mai da iskar gas, yayin da tsoron rikici tsakanin Amurka da Iran ya jawo tashin farashin mai a wannan makon.
Tashar na ɗaukar kashi ɗaya cikin huɗu na man fetur da ake jigila ta teku a duniya da kuma kashi ɗaya cikin biyar na dukkan iskar gas, bisa ga alƙaluman Hukumar Makamashi ta Duniya (International Energy Agency).