Matuƙan helikwaftan da ya faɗi kusa da Mashigar ruwan Hormuz suna “lafiya,” a cewar Shugaban Amurka Donald Trump .
Trump ya yi wannan kalaman ne ga manema labarai ranar Litinin da yamma bayan ya kalli wasan ƙarshe na gasar wasan ƙwallon kwando na NBA a birnin New York yayin da yake filin jiragen sama na ƙasa da ƙasa na John F. Kennedy.
Jaridar The New York Times ce ta fara ba da rahoton cewa wani jirgi mai sauƙar angulu na sojin Amurka ya faɗi kusa da mashigar ruwan a cikin wani yanayin da ba a tantance ba.
Faɗuwar na zuwa ne bayan Iran da Isra’ila sun yi musayar wuta ranar Litinin , lamarin da ya yi barazana ga tattaunawar ƙarfafa yarjejeniyar tsagaita wuta da ke rawa game da yaƙin Iran .
Babu cikakken bayani nan take ko makaman Iran ne suka harbo jirgin ko ya samu matsalar na’ura ne ko kuma wata matsala ta daban ce ta janyo faɗuwar, in ji rahoton.
Fadar White House da Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka da kuma Cibiyar Tsaron Amurka ba su mayar da martani nan take ba ga buƙatar neman tsokaci da aka tura musu.















