| Hausa
DUNIYA
1 minti karatu
Trump ya saka harajin kashi 25 kan ƙasashen da ke kasuwanci da Iran
Trump ya ce harajin na Amurka zai shafi duk wata ƙasa da ta ci gaba da ƙulla alaƙar kasuwanci da Tehran.
Trump ya saka harajin kashi 25 kan ƙasashen da ke kasuwanci da Iran
Trump ya ce harajin zai shafi kowace kasa da ta ci gaba da hulda da Iran. / AP
13 Janairu 2026

Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar cewa duk wata ƙasa da ke hulɗa da Iran za ta fuskanci harajin kashi 25 cikin 100 kan duk wata hulɗar kasuwanci da za ta yi da Amurka, yana mai cewa matakin zai fara aiki nan-take.

A cikin wata sanarwa, Trump ya ce harajin zai shafi kowace ƙasa da ta ci gaba da hulɗa da Iran.

"Daga yanzun nan, duk ƙasar da ta yi hulɗa da Iran za ta biya harajin kashi 25 cikin 100 kan kowane kasuwanci da ta yi da Amurka," in ji Trump.

Masu AlakaTRT Afrika - Iran ta ce a 'shirye' take ta tattauna da Amurka amma kuma ta 'shirya wa yaƙi'

Ya ƙara da cewa hukuncin zai shafi dukkan hulɗar kasuwanci da Washington, yana mai bayyana cewa ba za a bayar da wata togaciya ba.

Trump ya sake nanata barazanar a cikin sanarwa da dama, yana mai jaddada cewa ƙasashen da ke hulɗa da Iran za su fuskanci harajin a duk wata hulɗa da Amurka.

Sanarwar ta nuna ƙaruwar matsin lambar tattalin arziki ta Trump, yayin da yake alaƙanta damar shiga kasuwar Amurka da bin ƙa'idojin cinikayyar da ta shafi Iran.

Rumbun Labarai
Saudiyya da Isra'ila za su Amurka don tattaunawa yayin da Trump ke tura jiragen yaƙi na ruwa Iran
WHO: Amurka ta fita daga Hukumar Lafiya ta Duniya bayan shekara 78
Masana kimiyya sun gano zanen shacin hannu 'mai shekara 67,800' a wani kogo a Indonesia
Ministan Wajen Saudiyya da takwarorinsa na Iran, Oman da Qatar sun tattauna kan zaman lafiyar yanki
Amurka ta dakatar da ba da bizar masu ƙaura ga 'yan Nijeriya da wasu ƙasashe 74
Wani sanatan Amurka ya yi gargaɗi kan ƙaruwar ƙyamar Musulunci da ƙin jinin Larabawa
An katse intanet da wayoyin hannu a Iran
Matar shugaban Turkiyya ta gana da shugaban UNRWA kan shirin buɗe ofis a Ankara
Sanatocin Republican 5 sun bi sahun 'yan Democrat don neman sake duba ikon yaki na Trump a Venezuela
An kashe ɗansanda a kusa da Tehran yayin da zanga-zanga kan matsin rayuwa ta mamaye ƙasar Iran
Erdogan da Anwar na son ƙarfafa alaƙar Turkiyya da Malaysia tare da fifita fannin tsaro
Trump ya sanya hannu kan takardar neman cire Amurka daga ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa da na MDD
Shugaban Rundunar Sojin Iran ya yi barazanar mayar da martani ga Trump da Netanyahu
Abin da ya sa ya kamata Afirka ta damu kan samamen da Amurka ta kai Venezuela
An sayar da kifi mai nauyin kilogiram 240 a kan Naira biliyan 4.5 ($3.2m) a Japan
Me zai faru ga takunkuman da Amurka ta sanya wa Venezuela bayan ta ɗauke Maduro
Tarayyar Afirka ta nuna 'damuwa', Afirka ta Kudu ta nemi a yi taron MDD da gaggawa kan Venezuela
Trump ya gargaɗi Colombia, ya nufi Cuba bayan ya kama Maduro
Amurka ba za ta bari kowa ya ci gaba daga inda Maduro ya tsaya ba - Trump
Martanin duniya na karuwa kan hare-haren da Amurka ta kai wa Venezuela