| hausa
TURKIYYA
2 minti karatu
Erdogan ya yi gargaɗi kan cewa sake maimaita kisan kiyashi zai haifar da 'babban martani'
"Dole ne a bai wa zaman lafiya dama, dole ne a guji duk wasu ayyuka na zagon-ƙasa," in ji Shugaba Recep Tayyip Erdogan.
Erdogan ya yi gargaɗi kan cewa sake maimaita kisan kiyashi zai haifar da 'babban martani'
Shugaban ya yi wannan gargaɗin ne a ranar Juma'a
10 Oktoba 2025

Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, ya yi gargaɗi a ranar Jumma’a cewa komawa ga “yanayi na kisan kiyashi” a Gaza zai haifar da “babban martani,” yayin da yake maraba da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da Hamas.

An cim ma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da Hamas a safiyar Alhamis a Sharm el-Sheikh na Masar, bisa shirin matakai 20 da Shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar.

Mataki na farko na shirin ya hada da tsagaita wuta nan take, sakin wadanda aka yi garkuwa da su da fursunoni, janyewar Isra’ila zuwa layin da aka amince da shi a Gaza, da kuma isar da tallafin jin kai zuwa Gaza tare da goyon bayan kasa da kasa don sake gina yankin.

Yayin da yake jawabi a wani biki na kaddamar da sabbin gine-gine da ayyuka a lardin Rize na Tekun Bahar Maliya, Erdogan ya bayyana cewa Turkiyya ta yi — kuma za ta ci gaba da yin — duk mai yiwuwa don taimakawa wajen dawo da zaman lafiya, tsaro, da kwanciyar hankali a Gaza “da wuri-wuri.”

‘A daina zubar da jini’

Da yake magana kan yarjejeniyar tsagaita wuta, Erdogan ya jaddada cewa “abin da ya fi muhimmanci yanzu shi ne tabbatar da cewa an aiwatar da yarjejeniyar yadda ya kamata,” yana mai cewa Ankara za ta taka rawa mai muhimmanci a wannan tsari.

“Yankinmu, musamman Gaza, ya sha wahala sosai daga zubar da jini, kisan gilla, da hawaye,” in ji shi. “Dole ne a ba zaman lafiya dama, kuma a guji duk wani abu da zai kawo cikas.”

Erdogan ya bayyana yarjejeniyar a matsayin “babban mataki” zuwa ga zaman lafiya mai ɗorewa duk da ƙalubalen da ke gaba. “An buɗe ƙofar zaman lafiya ta dindindin a Gaza,” in ji shi. “Muna cewa — a daina zubar da jini.”

Amurka ta tabbatar cewa sojojin Isra’ila sun kammala janyewa zuwa layin rawaya a mataki na farko. Bisa yarjejeniyar, Hamas za ta saki mutane 20 da aka yi garkuwa da su tare da mayar da gawarwaki 28, yayin da Isra’ila za ta saki fursunonin Falasdinawa 250 da ke da hukuncin daurin rai da rai da kuma mutane 1,700 da aka kama tun ranar 7 ga Oktoba, 2023.

Rumbun Labarai
Turkiyya na jimamin tunawa da rasuwar Ataturk shekara 87 da suka wuce
Nasarar da aka samu a yankin Karabakh na Azerbaijan babbar nasara ce ga yankin Caucasus: Erdogan
Turkiyya ta yi umarnin kama Firaministan Isra'ila Netanyahu da wasu mutane kan kisan kiyashi a Gaza
Turkish Airlines ya sayi hannun jari na dala miliyan 355 a kamfanin Air Europa na Spain
Erdogan ya yi Allah wadai da kashe fararen-hula a birnin Al Fasher na Sudan
Za a gudanar da tattaunawa a Istanbul kan yarjejeniyar tsagaita wutar Gaza da matsalolin jinƙai
Tsarin duniya na yanzu ya fi ba da fifiko kan iko fiye da adalci: Babban Daraktan TRT Sobaci
Hamas ba ta da nukiliya, amma Isra'ila na da su: Erdogan ya nemi Berlin ta ɗauki mataki kan Tel Aviv
Ana shirin fara taron TRT World Forum karo na 9 a Istanbul
Cikin hotuna: Yadda aka yi bukukuwa a duk faɗin kasa na cikar Ranar Jamhuriya ta Turkiyya ta 102
Turkiyya ta yi kira a tsagaita wuta nan-take a yaƙin da ake yi a birnin Al Fasher, Sudan
Turkiyya za ta mika wa dakarunta tankar yaki ta Altay da aka samar da yawa a karon farko
Kungiyar ta'addanci ta PKK ta sanar da janyewa baki ɗaya daga Turkiyya
Babu wani lissafin siyasa ko na tsaro da zai yiwu a duniya ba tare da Turkiyya ba: Erdogan
Rumfar Karfe: Fasahar Turkiyya ta cikin gida mai aiki da Ƙirƙirarriyar Basira a sabon zamanin tsaro
Shugaba Erdogan ya shirya ziyartar yankin Gulf don haɓaka alaƙar tattalin arziki da ƙawance
Turkiyya ta yi maraba da yarjejeniyar tsagaita wutar Afghanistan da Pakistan
An Fara Taron Yaki da Shara na ‘Zero Waste’ a Istanbul karkashin jagorancin Emine Erdogan
Matar Shugaban Turkiyya Emine Erdogan ta yi kira a bunkasa shigar mata cikin harkokin duniya
Cinikayya tsakanin Turkiyya da Afirka ta wuce $37b ana sa ran ta kai $40b a 2025: Minista