Rundunar Sojin Nijeriya ta Operation Hadin Kai (OPHK) da ke yaƙar ta’addanci a arewa maso gabashin Nijeriya, ta bayyana cewa dakarunta sun daƙile hare-haren ‘yan ta’adda inda suka sa ‘yan ta’addan suka tafka asara.
Wata sanarwa da kakakin Operation Hadin Kai, Laftanal Kanal Sani Uba ya fitar ta ce ‘yan ta’addan sun kai hare-haren kan sansanonin sojin da ke Pulka da Mandaragirau ne ranar 14 ga watan Fabrairu da zummar ƙwace su.
“Sai dai kuma, ta hanyar jajircewa a yaƙi da ƙarfin soji da dabarun hangen nesa dakaru sun riƙe ƙasa kuma sun sa maharan sun tafka asara tare da sake tabbatar da rinjayar OPHK a faɗin fagen yaƙin,” in ji sanarwar.
Kazalika wasu ‘yan ta’addan Boko Haram/ISWAP sun fito daga dajin Sambisa kuma suka ƙaddamar da wani hari mai zafi kan dakarun da ke Pulka, in ji sanarwar.
“A wani martani da aka shirya da kyau, dakaru sun yi musayar wuta na tsawon lokaci da ‘yan ta’addan kuma suka daƙile harin tare da juya [yanayin harin],” in ji Laftanal Kanal Uba.
Duk da cewa maharan sun kutsa wani ɓangare na katange sansanin abin da ya sa aka lalata wasu kayayyakin aiki, sojojin da tallafin ƙarin jami’ai sun mayar da martani lamarin da ya sa ‘yan ta’addan suka tsere a gigice zuwa ta dajin Sambisa.
“Bayanan sirri masu tushe sun nuna cewa wasu ‘yan ta’addan sun rasa rayukansu ciki har da na wani babban kwamandansu da ake ce wa Abou Aisha wanda ya ji ciwo sakamaon harbi a wuya, lamarin da ya janyo mutuwarsa da rasa makamai da kayayyakin aiki,” in ji sanarwar.
Sanarwar ta ƙara da cewa babu sojan da ya rasu a harin da aka kai Pulka.
Kazalika ‘yan ta’addan sun kai hare-hare kan sansanin sojin da ke Mandaragirau, inda sojoji suka yi nasarar daƙile harin ba tare da ‘yan ta’addan sun iya kutsa cikin sansanin ba.
Sai dai kuma, sanarwar ta ce wasu jami’ai da ‘yan sa kai sun rasu yayin kare sansaninsu daga maharan.











