| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Yoweri Museveni ya sake lashe zaɓen shugaban ƙasar Uganda
Shugaban Uganda Yoweri Museveni ya lashe zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar a ranar Alhamis bayan hukumar zaɓen ƙasar ta sanar da shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasar.
Yoweri Museveni ya sake lashe zaɓen shugaban ƙasar Uganda
Wannan nasara ta ba shi damar tsawaita mulkinsa na kimanin shekaru 40 a kasar gabashin Afirka. / Yoweri Museveni
17 Janairu 2026

Shugaban Uganda, Yoweri Museveni, ya lashe zaɓen shugaban ƙasar a ranar Asabar domin fara wa'adi na bakwai bayan wani zabe da aka yi mai cike da ce-ce-ku-ce.

Hukumar zaɓen ta ce Museveni, mai shekaru 81, ya samu kashi 71.65 na kuri'u a zaben ranar Alhamis.

Jam'iyyarsa mai mulki ta National Resistance Movement (NRM), na kan gaba a kujerun ‘yan majalisa kamar yadda sakamakon wucin-gadi ya nuna.

Wannan nasara ta ba shi damar tsawaita mulkinsa na kimanin shekaru 40 a kasar gabashin Afirka.

Masu AlakaTRT Afrika - Shugaban Uganda Museveni na kan gaba sosai a sakamakon farko na zaɓe

Ya doke Bobi Wine, mai shekaru 43, tsohon mawaki da ya koma ɗan siyasa, wanda ya samu kashi 24.72% inda a ranar Asabar ya ce ya ɓoye bayan rundunar tsaro ta kai hari gidansa.

Abokin hamayya a gudu

Ya bayyana “cikakken kin amincewa da sakamakon bogi' kuma ya ce yana gudu bayan farmakin gidansa a daren Jumma'a.

“Ina so in tabbatar da cewa na samu tserewa daga hannunsu,” kamar yadda Wine ya wallafa a shafinsa na X a ranar Asabar. “A halin yanzu, ban kasance a gida ba, duk da cewa matata da wasu 'yan uwa an yi musu daurin-talala a gida.”

“Na san waɗannan masu laifin na nemana a ko'ina kuma ina ƙoƙarin yin iya bakin ƙoƙarina don samun tsaro,” in ji shi.

Kamfanin dillancin labarai na AFP ya ruwaito cewa jami'an 'yan sanda sun yi yawa a kewaye da babban birnin Kampala.

Yan sanda sun musanta cewa sun kai hari gidansa amma sun ce suna “kula da wuraren da muke ganin suna buƙatar tsaro”, inda suka ƙara da cewa suna kyautata zaton har yanzu jagoran ‘yan adawan yana gida.

“Ba mu tabbatar da cewa mun hana mutane zuwa wurinsa ba gaba ɗaya, amma ba za mu yi haƙuri da lokuta inda mutane ke amfani da gidansa don taruwa da... tada tunzura a yi tashin hankali ba,” in ji kakakin 'yansandan Kituuma Rusoke ga 'yanjarida.

Rumbun Labarai
Harin RSF na watan Oktoban 2025 a Al-Fasher na Sudan ya kashe aƙalla mutum 6,000: Rahoton MDD
AU: Shugabannin Afirka sun ƙaddamar da taron Ƙungiyar Tarayyar Afirka da batun ruwa da sauyin yanayi
Afirka ce kan-gaba wajen faɗaɗa samar da lantarki ta hasken rana a shekarar 2025: Rahoto
Gwamnatin Ghana ta ba da umarnin sarrafa kashi 50 cikin 100 na koko a cikin ƙasar
Sudan: Aƙalla mutum 21 sun mutu a hatsarin kwale-kwale a Kogin Nilu
Kasashe shida sun shiga Kwamitin Tsaro na Tarayyar Afirka
RSF ta kashe ƙananan yara a harin da ta kai wani masallaci a yankin Kordofan na Sudan
Saudiyya ta yi tur da RSF kan munanan ayyukanta a Al Fasher, ta buƙaci a ba da hanyar kai agaji
Mutum biyar sun mutu a hatsarin helikwaftan ɗaukar marasa lafiya a Libya
Yadda 'yan Somaliya suka gina wa tsohon shugaba ƙasarsu Farmaajo sabon gida
Sake dawo da ainihin martabar Afirka
RSF ta Sudan ta kai hari da jirgi maras matuƙi, ta kashe gomman mutane da yara
Dubban ‘yan kasar Libya sun taru don halartar jana'izar Saif al-Islam Gaddafi
Harin RSF a wani asibiti a Sudan ya kashe mutum 22, ciki har da ma'aikatan jinya
Ghana da Zambia sun ƙulla yarjejeniyar shiga ƙasashen juna ba tare da biza ba yayin ziyarar Mahama
Saif al-Islam Gaddafi: An kashe ɗan marigayi shugaban Libya Muammar Gaddafi
Afirka na fuskantar tarnaƙin bashin dala biliyan 90 a 2026, in ji S&P
Yadda Biteye na Senegal ke amfani da ƙwallon ƙafa don samun waraka ga ƙwaƙwalwa
Sojojin Rasha sun taimaka wajen daƙile hari a filin jirgin saman Nijar: Moscow
'Yanbindiga sun kashe sojojin Libya uku a kusa da kan iyakar Nijar