| Hausa
AFIRKA
3 minti karatu
Gidauniyar Turkiyya ta ba da tallafin abinci ga iyalai 8,250 da iftila’in fari ya shafa a Somaliya
Somaliya na fuskantar ƙarin matsalar tsaron abinci da rashin abinci mai gina jiki, inda kimanin mutane miliyan 6.5 ke fuskantar tsananin yunwa.
Gidauniyar Turkiyya ta ba da tallafin abinci ga iyalai 8,250 da iftila’in fari ya shafa a Somaliya
Tun daga shekarar 2017, EU ta samar da tallafin jinƙai na fiye da dala miliyan 817 ga Somaliya, in ji sanarwar. / TRT Afrika Hausa
27 Fabrairu 2026

Wata kungiyar agaji ta Turkiyya ta kai tallafin abinci ga iyalai 8,250 a yankunan da fari ya shafa a Somaliya a lokacin watan Ramadan mai tsarki, in ji jami'an Turkiyya.

Gidauniyar Turkiyya Diyanet (TDV) ta rarraba kayan abinci a jihohi bakwai da yankuna 13 na ƙasar Somaliya a matsayin wani bangaren shirinta na ba da agaji a watan Ramadan, wanda ke samun gudummawa daga masu ba da sadaƙa.

An shirya kayan tallafin ne ga iyalai da ke fama da matsalar tattalin arziki a yanayi iftila’in fari mai da aka kwashe tsawon lokaci ana fuskanta kana ya kara muni a 'yan shekarun nan.

Tawagogi da suka kunshi ma'aikatan gidauniya da masu sa kai ne suka yi rabon kayan abinci a yankuna daban-daban, ciki har da sansanonin da ke babban birnin Mogadishu.

An gudanar da tarukan ba da tallafin a sansanin Hindere da ke gundumar Daynile da kuma sansanin Bilhayr da ke yankin Garapaley, inda jami'ai suka gana da iyalai da lamarin ya shafa bayan sun ƙarbi kayayyakin.

Omer Faruk Arslan, mai ba da shawara kan ayyukan addini a Ofishin Jakadancin Turkiyya da ke Mogadishu, ya ce tallafin jinƙan yana da matukar muhimmanci yayin da iftila’in fari ya yi tsanani a fadin Somaliya.

"A cikin shekaru 2, an samu matsaloli masu tsanani a fannin samun abinci da ruwa sakamakon fari," in ji Arslan "amma ta hanyar tallafin masu ba da sadaka, muna kaiwa masu buƙata kayan abinci yankuna 13."

Tallafin EU ga Somaliya

A ranar Alhamis, ƙungiyar Tarayyar Turai (EU) ta sanar da ba dala miliyan 74 a matsayin tallafin jinƙai don tallafawa al'ummomin da ke cikin mawuyacin hali a faɗin Somaliya yayin da ƙasar ke fama da iftila’in "fari mai tsanani, da kuma rikice-rikicen da ake ci gaba da fuskanta, gami da ƙaura da kuma hauhawar farashin abinci."

A wata sanarwa da ta fitar, ƙungiyar EU ta ce tallafin zai fi mayar da hankali wajen ayyukan ceton rai, gami da na kiwon lafiya da abinci masu gina jiki, da tallafin kuɗi na gaggawa, da ayyukan ruwa da tsaftar muhalli, da shirye-shiryen kariya, da kuma ilimin gaggawa.

Somaliya na fuskantar ƙarin matsalar tsaron abinci da rashin abinci mai gina jiki, inda kimanin mutane miliyan 6.5 ke fuskantar tsananin yunwa, a cewar sanarwar.

Binciken jinƙai ya nuna cewa kimanin yara miliyan 1.85 'yan ƙasa da shekara biyar suna cikin haɗarin kamuwa da tsananin matsalar rashin abinci mai gina jiki.

EU ta ce za a bayar da taimakon ta hanyar abokan hulɗa na jinƙai da aka amince da su waɗanda ke aiki a ƙasa don tabbatar da cewa taimakon ya isa ga waɗanda abin ya cancanta akan lokaci, tare da haɗin kai da kuma aminci.

Tun daga shekarar 2017, EU ta samar da tallafin jinƙai na fiye da dala miliyan 817 ga al’ummar Somaliya, in ji sanarwar.

Rumbun Labarai
Yadda yakin Iran ke shafar tattalin arziki, yanki da siyasar Afirka
Za a cim ma yarjejeniyar bututun gas na Nijeriya-Maroko kan biliyan $25 a bana: Jami'i
Fafaroma Leo ya fara ziyararsa ta farko zuwa Afirka
Matsalar yunwa a Sudan: Miliyoyin mutane na cin abinci sau ɗaya a rana
Ana gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Jamhuriyar Benin
Shugaban ƙasar Djibouti Guelleh ya sake yin nasara karo na shida
Ana gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Djibouti inda Guelleh da ke mulki ke neman wa'adi na shida
Daga hanyoyin mulkin mallaka zuwa na korar mutane: Afirka da siyasar korar baƙi daga wata ƙasa
Yadda ajujuwan Afirka ke fuskantar jarrabawa mafi tsauri a duniya
Kamaru ta ce ‘yan kasarta 16 sun mutu yayin taya Rasha yaki da Ukraine
Dalilin da ya sa Kenya da Ethiopia suka zama manyan masana'antun furanni a duniya
Ambaliyar ruwa ta kashe mutane 15 a Angola
Senegal ta haramta wa jami'an gwamnati tafiye-tafiye marasa muhimmanci zuwa ƙasashen waje
Yadda aikin dala miliyan 240 ke bai wa al’umar gaɓar teku a Benin da Mauritania damar gwagwarmaya
Gwamnatin Madagascar ta daƙile yunƙurin kashe shugaban ƙasar Michael Randrianirina
Sudan ta yi Allah wadai da 'mummunan' harin da RSF ta kai wani asibiti yayin allurar rigakafin yara
Ghana za ta fara aiwatar da shirin shiga ƙasar ba tare da biza ba ga dukkan 'yan Afirka
Shugaban riƙon jihar Kudu maso yammacin Somaliya zai hau kan mulki bayan ajiye aikin shugaba
Sudan ta nemi 'yan ƙasar da suka yi ƙaura zuwa ƙasashen waje saboda yaƙi su koma gida
Hukumar leƙen asirin Somalia ta kashe masu haɗa bama-baman Al Shabab