| Hausa
NIJERIYA
1 minti karatu
Matatar mai ta Dangote ta fara dakon fetur kyauta zuwa wasu jihohin Nijeriya
A cewar kamfanin, wannan hidima ta sufurin mai kyauta ta shafi jihohin Legas da Ogun da Rivers da Kaduna da Delta da kuma Babban Birnin Tarayya, Abuja.
Matatar mai ta Dangote ta fara dakon fetur kyauta zuwa wasu jihohin Nijeriya
Matakin zai shafi jihohi biyar ne da babban birnin tarayyar kasar a karon farko / Reuters

Matatar Man Fetur ta Dangote ta fara dakon fetur kyauta zuwa jihohi shida a faɗin Najeriya, ciki har da babban birnin tarayyar ƙasar, Abuja.

Kamfanin ya sanar da wannan sabon shiri ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na dandalin sada zumunta na X a ranar Laraba.

A cewar kamfanin, wannan hidima ta sufurin mai kyauta ta shafi jihohin Legas da Ogun da Rivers da Kaduna da Delta da kuma Babban Birnin Tarayya, Abuja.

Kamfanin ya bayyana cewa wannan damar ta shafi abokan hulɗa ne kawai wadanda suka sayi akalla lita 50,000 ta man fetur.

Matakin na zuwa ne kakwanaki kaɗan bayan Matatar ta Dangote ta gana da masu ruwa da tsaki a fannin kasuwancin mai na ƙasa don tattaunawa kan samar da farashin fetur mai sauƙi da ya dace da kasuwa.

Taron ya kammala ne inda masu ruwa da tsakin suka nuna goyon bayansu ga yunkurin kara rage farashin man fetur.

Kafin wannan lokaci, kamfanin ya riga ya sanar da ragi na hudu a jere na farashinsa na sayar da fetur, inda ya dawo da shi N1,075 a kowace lita. 

Rumbun Labarai
Amurka ta aika sabbin kayayyakin soji Nijeriya
Zaben Nijeriya na 2027: Matakan Tinubu na rage talauci da alƙawarin Atiku na mayar da tallafin fetur
Jakadan Nijeriya ya ziyarci ’yan kasar 198 da ke gidan yari a Indiya
Mutane da dama sun mutu yayin da wasu ke asibiti bayan sun sha wani maganin gargajiya a jihar Ondo
Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya ta kama wasu mutane da kudade da ake zargin kuɗin fansa ne
'Yansandan Nijeriya sun kama mutum biyu kan zargin kashe Danshagamu a Kano
Nijeriya ta naɗa sabon kwamandan yaƙi da ƙungiyar ta’addanci ta Boko Haram
NEMA ta karɓi ’yan Nijeriya 180 da aka mayar da su gida daga Libya
Sojojin Nijeriya sun kama wasu da ake zargin masu kai wa ’yanta’adda kayayyaki ne a Jihar Yobe
FIFA ta tura tawaga zuwa Nijeriya don gano ko gwamnati ta tsoma baki a murabus ɗin shugabannin NFF
INEC za ta ƙaddamar da na’urar bibiyar shirye-shiryen zaɓe kai-tsaye
An  kashe mutum 12, an jikkata 2 a sabon harin da Boko Haram ta kai wani ƙauye a Adamawa ta Nijeriya
‘Yanbindiga sun kashe mutum 10, sun sace 40 a wani ƙauyen Sokoto
Gwamnatin Jihar Filato a Nijeriya ta rufe makarantu saboda ɓarkewar cutar mashaƙo
NDC ta yi watsi da jita-jitar da ake yaɗawa kan ba ta da ’yan takarar gwamna a jihohin Nijeriya 12
Sojojin Nijeriya sun ceto mutum 36 da aka sace a kasar, sun kuma halaka ’yanta’adda da dama
‘Yanbindiga sun kashe mutum biyar tare da jikkata uku a wasu ƙauyukan Sokoto
Shari'ar Tinubu a Amurka ta neman haƙƙi ce ba ta laifi ba ce— Fadar Shugaban ƙasa
Darakta Janar na DSS ya umarci jami'ansu da kar su kama kowa yayin da farar-hula suka samu sabani
Nijeriya ta musanta zargin goyon bayan yunƙurin 'juyin mulki' a Nijar