| Hausa
WASANNI
2 minti karatu
Ɗan wasan Ghana Semenyo ya koma Man City daga Bournemouth kan dala miliyan 87
Ɗan wasan gaban Ghana Antoine Semenyo ya ci ƙwallaye 10 kuma yana cikin 'yan wasan gaba mafi kyau a ƙwallon Turai a wannan kakar.
Ɗan wasan Ghana Semenyo ya koma Man City daga Bournemouth kan dala miliyan 87
Antoine Semenyo ya rattaba hannu kan yarjejeniyar shekara biyar da rabi. Hoto: Manchester City / Others
9 Janairu 2026

Manchester City ta sanya hannu domin sayen ɗan wasan gaban Ghana, Antoine Semenyo, daga Bournemouth a ranar Jumma'a domin ƙara ƙarfafa ‘yan wasan gaba a ƙoƙarin ƙungiyar na neman kambin Premier League da Champions League.

Semenyo, wanda ya zura ƙwallaye 10 kuma ya kasance ɗaya daga cikin 'yan gaba mafiya ƙwarewa a ƙwallon kafa ta Ingila a wannan kakar, ya koma a kan yarjejeniya da ake cewa ta kai fam miliyan 65 (kimanin dalar Amurka miliyan 87) kuma yarjejeniyar ta yi tsawon shekaru biyar da rabi.

A halin yanzu zai shiga cikin jerin ‘yan gaban City waɗanda suka haɗa da Jeremy Doku, Omar Marmoush, Savinho da Oscar Bobb. Savinho da Bobb a halin yanzu suna jinya, yayin da Marmoush — wanda yake halartar Gasar Cin Kofin Afirka — bai samu farin jini a wannan kakar ba.

Semenyo mai shekaru 26 an kuma danganta shi da Manchester United da Liverpool. Ya shafe kaka biyu da rabi a Bournemouth bayan ya koma daga Bristol City.

“Ina da babbar dama ta ingantawa, ” kamar yadda Semenyo ya ce a cikin wata sanarwa ta City, don haka kasancewa a wannan kulob, a wannan matakin na aikina, ya dace sosai da ni. Girmamawa ce a kasance a nan.

“Mafi kyawun wasan ƙwallona zai zo nan gaba, na tabbata da hakan.

Rumbun Labarai
Kwana 500 babu aski: Yadda sumar Frank Ilett ta zama shaidar matsalar Man United
Toni Kroos ya soki gasar ƙwallo ta Saudiyya game da raina tasirin Ronaldo
Victor Osimhen ya ci ƙwallo ta 200 a rayuwarsa ta wasa
Atletico Madrid ta ce ta cim ma yarjejeniya da Atalanta kan ɗanwasan gaban Nijeriya Ademola Lookman
Real Madrid za ta sake karawa da Benfica a wasan cike gurbi na Gasar Zakarun Turai
Mourinho ya bai wa Kocin Real Madrid haƙuri bayan Benfica ta doke Madrid a Gasar Zakarun Turai
CAF ta dakatar da kocin Senegal da Achraf Hakimi
Cole Palmer na son komawa Man United, Liverpool ba za ta rabu da kyaftin dinta, Virgil van Dijk ba
'Yanwasan Senegal sun samu kyautar kuɗi da fuloti saboda lashe Kofin AFCON
Dubban mutane sun halarci bikin karrama Zakarun Kofin AFCON a Senegal
Real Madrid ta sallami Xabi Alonso, ta nada Alvaro Arbeloa sabon koci
Hukumar CAF ta yi tir da rashin ɗa'a a zagayen kwata-fainal na AFCON 2025
Yadda ƙarin kuɗaɗen tallafi ke taimaka wa mata ‘yanwasan ƙwallon ƙafa da ke fama da nakasa a Kenya
Wane ne Liam Rosenior, sabon kocin Chelsea?
Manchester United ta kori kocinta Ruben Amorim bayan ya soki shugabancin kungiyar
An sallami Anthony Joshua daga asibiti
Abubuwa 5 game da mai jiran Man United ta ci wasa 5 a jere, wanda ya kwana 452 ba aski
Yadda Tanzania ta tsallaka gaba da maki biyu kacal a gasar AFCON 2025
Hatsarin mota ya rutsa da Anthony Joshua a jihar Ogun ta Nijeriya
AFCON 2025: Za a fara wasannin ƙarshe na matakin rukuni don tantance ƙasashe 16 masu tsallakawa gaba