| Hausa
WASANNI
3 minti karatu
Masar ta shigar da ƙorafi gaban FIFA kan alƙalin wasa bayan nasarar Argentina kanta
Shugaban Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Masar ya nemi a binciki gabaɗaya tawagar alƙalai, ciki har da alƙalan bidiyo, saboda kurakuran da suka yi ɓaro-ɓaro.
Masar ta shigar da ƙorafi gaban FIFA kan alƙalin wasa bayan nasarar Argentina kanta
Alkalin wasa Francois Letexier yana nuna wa kocin Masar Hossam Hassan katin rawaya. / REUTERS

Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Masar ta sanar ranar Laraba cewa ta nemi a kori tawagar alƙalan da suka jagoranci wasan da Masar ta yi rashin nasara a hannun Argentina da ci 2-3 a wasan zagaye na ‘yan-16 a Gasar Kofin Duniya.

"Hany Aburida, Shugaban Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Masar, ya shigar da ƙorafi gaban FIFA, yana neman a gudanar da bincike kan alƙali ɗan Faransa, Francois Letexier…, bayan manyan kurakuran alƙalanci da tawagar alƙalai ta aikata da nuna bambanci, wanda ya sa Masar ta yi rashin nasara a wasan, kuma ta fice daga Gasar Kofin Duniya," in ji wata sanarwa daga hukumar.

A daren Talata, Letexes ya soke ƙwallon da Mostafa Ziko ya ci lokacin da suke gaban Argentina da ci 1-0, sakamakon duban da VAR da gano an yi wa Lisandro Martínez ƙeta daga fari.

Minti kaɗan bayan haka, Ziko ya kai Masar gaba da ci 2-0 kuma ta kasance a gaban har zuwa matakin ƙarin lokaci inda aka samu hatsaniya, bayan Cristian Romero da Lionel Messi suka rama ƙwallayen biyu.

Neman yin bincike

Gabanin ƙwallon da ta bai wa Argentina nasarar ta hannun Enzo Fernández, Masar ta yi imanin ya kamata a ce an ba su fanareti saboda jan da Alexis Mac Allister ya yi wa Hamdy Fathy.

"Aburida ya nemi a binciki dukan tawagar alƙalan, ciki har da alƙalan fasahar bidiyo, saboda kura-kurai bayyanannu da kuma ƙin duba wasu daga cikin hotunan da muke ganin suna goyon bayan tawagar ƙwallon ƙafa ta Masar, kuma muna ganin a cikinsu haƙƙin tawagar 'Pharaohs' ne samun halastacciyar ƙwallo da kuma fenareti," in ji sanarwar ta Masar.

Sanarwar ta ƙara da cewa shugaban ya kuma "nemi a cire alƙalin da dukan tawagar daga Gasar Kofin Duniya, bayan gudanar da bincike kan waɗannan kurakurai da kuma tabbatar da laifin nuna bambanci kan tawagar ƙasar Masar".

Sanarwar ta dace da maganganun mai horar da Masar, Hossam Hassan, da ya yi nan-take bayan wasan.

“An yi mana maguɗi”

Hassan ya shaida wa 'yan jarida cewa, "Ba na son in lulluɓe magana na ce mun yi rashin sa'a. An yi mana maguɗi yau, mun sha rashin adalci".

"Ba mu ga girmamawa ko nuna adalci ba. Babu girmamawa ko nuna adalci."

Hassan ya shaida wa shafin BeIN cewa, "Wataƙila suna son su bar zakarun duniya [na bara, Argentina] a gasar ne. Wataƙila suna son Messi ya ci gaba da kasancewa a gasar."

"A ƙwallon ƙafa, wani lokaci akwai abubuwa daga waje da ke shafar wasan fiye da fannoni ƙwarewa. Zakarun duniya sun samu goyon baya a kowane mataki."

Rumbun Labarai
Danwasan Chelsea, Mudryk, ya dawo kwallo bayan dakatarwar kwana 600 bisa laifin shan kwayoyin kuzari
Arsene Wenger ‘ba shi da masaniya’ kan shirin Infantino na sayar da hannun-jarin Gasar Kofin Duniya
FIFA ta gaza hukunta Isra'ila kan karya dokokinta, a cewar hukumar Kwallon Kafa ta Falasɗinu
Masu adawa da Infantino sun yi barazanar gudanar da gasar kofin duniya ba a karkashin FIFA ba
WAFCON: Tawagar Super Falcons ta Nijeriya mai 'yanwasa 10 ta doke Zambia
Infantino ya ce FIFA ta fasa shirin sayar da hannayen-jari na Kofin Duniya ga ‘yan kasuwa
FIFA ta ce 'babu wanda zai sayar da ƙwallon ƙafa'
UEFA ta sha alwashin ƙaurace wa FIFA idan aka ci gaba da shirin sayar da Gasar Kofin Duniya
Infantino ya goyi bayan ƙudurin saka hannun jari na FIFA, ya ce 'dama ce ta musamman'
UEFA ta soki shirin Infantino na $4.2bn don zuba jari a Gasar Kofin Duniya ta FIFA
An nada Zinedine Zidane a matsayin sabon kocin tawagar kwallon kafa ta Faransa
Yan Diomande ne zai kasance dan Ivory Coast na farko da zai buga wa Real Madrid wasa
Real Madrid ta sanya fam miliyan 137 kan Vinicius Junior
Lamine Yamal: Gwarzon Kofin Duniya na Spain ɗan asalin Moroko da Equatorial Guinea
Norway za ta shigar da ƙara ga hukumar FIFA game da ce-ce-ku-ce kan jan katin Balogun
Real Madrid na farautar zakaran kofin duniya Ferran Torres daga wajen Barcelona
Yadda goyon bayan Falasɗinu ya haɗa kan Musulmai suka goyin bayan Spain a Gasar Kofin Duniya na 2026
Sifaniya ta zama ƙasa ta farko da ta riƙe Kofin Duniya na maza da na mata, da kofin nahiya a tare
An sayar da jesin da Pele ya saka a wasan ƙarshe na Kofin Duniya a 1958 kan $4.9m
Likitan tawagar Senegal 'likitan mata' ne, in ji shugaban hukumar kwallon kasar