Lokacin da David Sacks, fitaccen mai zuba jari a Silicon Valley kuma mai zuba jari dan jari hujja - wanda shugaban Amurka Donald Trump ya naɗa a matsayin babban jami'in kula da Kirkirarriyar Basira da Kudin Kirpto na Fadar White House - ya yi gargaɗin cewa Isra'ila na iya la'akari da amfani da makaman nukiliya a kan Iran idan rikicin ya ƙaru, wataƙila a karon farko ne wani babban jami'in Amurka ya amince a fili cewa Isra'ila tana da makaman nukiliya kuma za ta iya amfani da su a yaƙin.
Sacks, wanda ba wai jami'in tsaro ba ne, shi ma ya ba da shawarar Amurka "ta ayyana nasara da kuma fita" daga yaƙin Amurka da Isra'ila da Iran.
Trump ya mayar da martani ga furucin mai ba shi shawara game da amfani da makaman nukiliya da Isra'ila za ta iya yi, yana mai cewa: "Isra'ila ba za ta yi hakan ba. Isra'ila ba za ta taɓa yin hakan ba."
Duk da haka, Sacks ba shi ne kaɗai ya yi gargaɗi kan yaƙin nukiliya a Gabas ta Tsakiya ba.
A wata hira da ya yi da Middle East Eye, John Mearsheimer, wani masanin kimiyyar siyasa na Amurka kuma masanin hulda da kasashen duniya, ya yi gargadin cewa: "Idan Isra'ilawa suka sha kashi a Iran ... za su san cewa za su fusata al'ummar Iran. Za su san cewa Iran mai makaman nukiliya za ta kasance mai matukar hatsari daga mahangar Isra'ila."
"Idan ba za su iya hana hakan ta hanyar da aka saba gani ba, to za mu kai ga wani yanayi inda suke tunanin amfani da makaman nukiliya. Kuma kamar yadda muka sani, babu wata ƙasa a duniya da ta fi ta rashin tausayi."
Theodore Postol, farfesa da ya yi ritaya a MIT kuma ƙwararre kan tsarin tsaron makamai masu linzami, ya bayyana damuwa kai-tsaye cewa Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu zai iya amfani da makamin nukiliya a kan Iran idan an gama karar da duk wani zabi da yake da shi.
A wata hira da ya yi kwanan nan, ya yi gargaɗin cewa wannan na iya haifar da ramuwar gayya daga Iran, koda kuwa cewa Tehran dole ne Tehran ta hada nata cikin gaggawa.
Jami'an Hukumar Lafiya ta Duniya sun riga sun shirya don yiwuwar fuskantar bala’in nukiliya idan yaƙin ya tsananta.
Hanan Balkhy, Daraktar WHO ta gabashin Bahar Rum, ta shaida wa POLITICO cewa ma'aikatan Majalisar Dinkin Duniya na sa ido kan sakamakon hare-haren Amurka da Isra'ila a wuraren nukiliya na Iran kuma suna ci gaba da "yin taka tsan-tsan" ga kowace irin barazanar nukiliya.
"Mafi munin yanayi shi ne lamarin nukiliya, kuma wannan shi ne abin da ya fi damunmu," in ji Balkhy, tana mai ƙarawa da cewa ma'aikatan sun shirya tsaf don afkuwar harba makaman nukiliya, ciki har da ma kai hari kan cibiyar nukiliya ko amfani da makamin da kansa.
Harba nukiliya ba ya teburin tattauna gaba daya
Yayin da Iran ta yi alƙawarin ci gaba da gwabza yaƙi "har sai an yi nasara gaba ɗaya" kuma ta ƙi amincewa da buƙatun Amurka da Isra'ila, aƙalla a bainar jama'a, yayin da take ci gaba da adana tarin uranium ɗinta na kusa da zama makaman yaƙi, duk da haka, wasu masu sharhi suna ba da ganin cewa rikicin na yanzu ba zai iya rikidewa zuwa yaƙin nukiliya ba komai tsawon lokacin da yaƙin ya ɗauka.
"Zan iya cewa a tarihi, bisa ga shekaru 35 na gogewa da na yi a wannan fanni, barazanar amfani da makaman nukiliya ba shi da wani matsayi a yaƙin da ake yi a yankin Gabas ta Tsakiya ko kuma a cikin wani rikici, ganin cewa waɗannan makamai ne marasa ma'ana kuma na ta'addanci," kamar yadda Daryl G. Kimball, Babban Daraktan Ƙungiyar Kula da Makamai a Washington, ya shaida wa TRT World.
Kimball, wanda ke jagorantar bincike da fafutukar kare manufofin makaman nukiliya, sinadarai, da na halittu, a ƙungiyar da ke aiki don rage barazanar da makamai mafi hatsari ke haifarwa a duniya, ya ce: "Kodayake, Isra'ila da Amurka, waɗanda dukkan su ke da makaman nukiliya, suna iya jin takaicin cewa ba za a iya cim ma burinsu na yaƙi ta hanyar kai hari kan Iran da makamai da aka saba amfani da su ba, ya kamata a ɗauki yin amfani da makaman nukiliya a matsayin "batun da ba ya kan teburin tattaunawa" kuma ba za a ɗauke su a matsayin barazana mai inganci ba a cikin rikicin da ake ciki a yanzu."
Kusan makonni huɗu da fara yaƙin da Amurka da Isra'ila suka ƙaddamar a kan Iran, an kashe ɗaruruwan mutane, galibinsu fararen hula. An lalata kayayyakin more rayuwa na soja da na farar hula a Gabas ta Tsakiya, kasuwar mai ta ruguje, kuma tsaron yankin Tekun Fasha ya lalace.
Ko da Isra'ila ta kashe manyan shugabannin siyasa da na soja na Iran, kuma Amurka da Isra'ila suna kai hari kan kayayyakin makamashin Iran, ƙarfin faɗan Iran ya ci gaba da wanzuwa.
Tehran ta ci gaba da tura jiragen sama marasa matuƙa da makamai masu linzami kan Isra'ila, da sansanonin Amurka, da kayayyakin makamashin ƙawayenta na yankin Gulf. Tehran ta kuma nuna cewa hakan na iya kawo cikas ga zirga-zirgar mai ta hanyar mashigar teku ta Hormuz, babbar hanya ga kashi 20 cikin 100 na man da ake amfani da shi a duniya.
Yayin da NATO da ƙawayen Turai suka ƙi shiga yaƙin, Shugaban Amurka Trump ya nemi yin amfani da hanyar laluma da bambami, yana haɗa kai hare-hare da diflomasiyya don cim ma burinsa na yaƙi.
A ranar Litinin, Trump ya yi iƙirarin cewa gwamnatinsa tana tattaunawa da wani "babban mutum" a Iran game da yiwuwar cim ma sulhu.
Amma shugaban majalisar dokokin Tehran, Mohammad Bagher Ghalibaf ya bayyana cewa "babu wata tattaunawa" da ake yi, yana zargin shugaban Amurka da yin yaudara a fagen kasuwanni.
Pakistan na kokarin shiga tsakani kan tattaunawar Amurka da Iran. Wannan ya biyo bayan tabbatarwar hakan daga Fadar White House game da kira ta wayar tarho da aka yi tsakanin shugaban rundunar sojin Pakistan, Asim Munir, da Trump game da rikicin.
Yayin da Islamabad ta bayyana shirinta na samar da wurin tattaunawar zaman lafiya - wanda babu ɗayan ɓangarorin da suka sanar a hukumance - Isra'ila, tare da ƙasashen Gulf Bahrain, Kuwait, Hadaddiyar Daular Larabawa, da Saudiyya, suna ci gaba da samun sabbin hare-haren jiragen sama marasa matuƙa da makamai masu linzami daga Iran
Barazanar Nukiliya ba ta da tasiri wajen ‘tankwara’ makiya
Yayin da yaƙin ke ci gaba, Kimball ya yi imanin cewa barazanar da ƙasashe ke yi na amfani da makaman nukiliya kan ƙasashen da ba su da nukiliya ba ta da tasiri wajen canza matsayinsu.
"Tarihi ya nuna cewa barazanar nukiliya da Amurka da sauran ƙasashen da ke da makaman nukiliya ke yi wa ƙasashen da ba na makaman nukiliya ba ba ta da tasiri wajen tilasta musu halayensu ko tilasta musu yin saranda," in ji shi.
Duk da haka, Kimball ya yi gargaɗin cewa Trump da Netanyahu duka suna da iko na musamman, wanda ba shi da iyaka don ba da izinin amfani da makaman nukiliya.
"Trump da Netanyahu suna aiki ne a ba tare da kallon dokokin ƙasa da dokokin ƙasa da ƙasa ba, gami da Dokar Yaƙi da Makamai, kuma kowane mutum daga cikin su biyun na da ikon da ba a tantance ba na ba da umarnin amfani da makaman nukiliya."
Mutanen da suka mutu sakamakon rikicin ya zuwa yanzu sun haura 1,500 a Iran da kuma 1,000 a Lebanon. Isra'ila ta ba da rahoton mutuwar mutane 15, tare da ma'aikatan sojan Amurka 13 da fararen hula na yankin Gulf. Hare-haren da Amurka da Isra'ila suka kai a Iran da kuma mamayar da ƙasar Isra'ila ta yi a kudancin Lebanon sun raba miliyoyin mutane da muhallansu.
Ko wannan yaki ya zo karshe da tsagaita wuta na dindindin, ko tsawaita lokacin dakatarwa, ko kuma ƙaruwar rikici, wasu masu sharhi na jayayyar cewa yiwuwar rikicin nukiliya "yana baya-baya" a Gabas ta Tsakiya.
"Ina ganin hatsarin Amurka da yiwuwar amfani da makaman nukiliya da Isra'ila za ta iya yi don kawo ƙarshen rikicin ya kasance ba abun da zai yiwu ba. Washington ta dage cewa hare-haren da ta saba kai wa suna samun nasara, kuma jami'an Isra'ila sun yi hasashen ƙarin makonni. Babban ƙalubalen da Amurka ke fuskanta yanzu shi ne sake buɗe mashigar Hormuz kuma hare-haren nukiliya ba zaɓi ba ne mai kyau ga hakan, ko da kuwa an bar ƙin amincewa ta ɗabi'a da siyasa. Don haka, ina tsammanin za a iya guje wa wannan mummunan yanayi," in ji Richard Gowan, daraktan shirye-shirye tare da Ƙungiyar International Crisis Group yayin tattaunawa da TRT World.
Gowan, wanda ke kula da ayyukan Ƙungiyar kan siyasa ta ƙasashen waje, yanayin duniya a cikin rikici da haɗin gwiwa tsakanin ƙasashe, ya ce idan Amurka ta yi amfani da makaman nukiliya, za ta fuskanci Allah wadai a duniya kuma Larabawan Gulf za su kasance cikin waɗanda suka shiga cikin sukar.
"Har ma da ƙasashen da suka yi suka a kan yaƙin ba za su iya guje wa yin Allah wadai da amfani da makaman nukiliya ba. Kuma mutane da yawa na iya jin tsoron cewa Rasha ko China za su yi amfani da abin da ya gabata a nan gaba don ba da hujjar amfani da makaman nukiliya na kansu. Trump koyaushe yana da kyakkyawan tsoron yaƙin nukiliya, kuma da wuya ya bi wannan hanyar duk da dukkan maganganunsa na ban dariya," in ji shi.















