DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
Qatar tare da Amurka da Tarayyar Afirka sun shafe watanni suna gudanar da jerin tattaunawa don kawo ƙarshen rikici a gabashin DRC mai arzikin ma'adinai, inda M23 ta ƙwace manyan birane.
Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo da 'yan tawayen M23 sun rattaɓa hannu kan wata yarjejeniyar da nufin samar da zaman lafiya da kuma kawo ƙarshen yaƙi.
An sanya hannu kan yarjejeniyar a ranar Asabar wadda wakilai daga ɓangarorin biyu suka saka hannu wa a wani taro a babban birnin Qatar, Doha.
Qatar tare da Amurka da Tarayyar Afirka sun shafe watanni suna gudanar da jerin tattaunawa don kawo ƙarshen rikici a gabashin DRC mai arzikin ma'adinai, inda M23 ta ƙwace manyan birane.
‘Yan tawayen na M23 a wani mataki da suka ɗauka na baya-bayan nan da goyon bayan maƙwabciyar Kongo wato Rwanda, sun ƙwace birnin Goma a watan Janairu, birni mafi girma a gabashin DRC, inda suka ci gaba da ƙwace wasu garuruwa a lardunan Kivu ta Arewa da Kivu ta Kudu.
Tun bayan sake ɗaukar makami a ƙarshen 2021, rukunin M23 ya ƙwace manyan yankuna a gabashin DRC tare da tallafin Rwanda, abin da ya haddasa mummunan rikicin jinƙai.
Rwanda ta musanta cewa tana tallafa wa M23
A yayin bikin ƙulla yarjejeniyar a Doha, babban mai sulhu na Qatar, Mohammed Al-Khulaifi, ya kira yarjejeniyar "ta tarihi", yana mai cewa masu shiga tsakani za su ci gaba da ƙoƙari don tabbatar da zaman lafiya a fagen.
Dubban mutane sun mutu a wani farmaki da M23 ta kai a watan Janairu da Fabrairu, wanda a ciki kungiyar ta kwace manyan biranen lardi na Goma da Bukavu.
Yarjejeniyar watan Yuli da aka sanya wa hannu a Doha ta biyo bayan wata ta daban, yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin gwamnatocin DRC da Rwanda da aka rattaɓa wa a Washington a watan Yuni.
Qatar ta karɓi baƙuncin tattaunawa daban-daban tsakanin gwamnatin DRC da M23 tun watan Afrilu.
A watan Oktoba, sun cim ma yarjejeniya kan yadda za a sa ido a kan tsagaita wuta