AFIRKA
2 minti karatu
Ayyukan da sojojin Nijar suke yi a yankin Tillaberi sun fara tasiri: Shugaba Tiani
Shugaba Tiani ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ziyara Jihar Tilleberi inda ya yi rangadin dakarun da ke jihar wadda ke fama da matsalar tsaro.
Ayyukan da sojojin Nijar suke yi a yankin Tillaberi sun fara tasiri: Shugaba Tiani
Shugaban Nijar ya kai ziyarar aiki jihar Toilleberi da ke fama da hare-haren 'yan ta'adda
6 Oktoba 2025

Shugaban ƙasar Nijar Janar Abdourahamane Tiani ya shaida wa jami’an tsaron runduna ta 9 mai suna “Operation Niya,” cewa “ayyukan da kuke yi kullum sun fara tasiri.”

Shugaba Tiani ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ziyara Jihar Tilleberi inda ya yi rangadin dakarun da ke jihar wadda ke fama da matsalar tsaro.

Janar Abdourahamane Tiani ya taya dakarun tsaron murna game da gagaruman ƙoƙarin da suke yi a ko wace rana kan tabbatar da yanayi na tsaro domin amfanin dukkan al’umma.

 "Aikin da kuke yi a ko wace rana ya fara tasiri," kamar yadda kamfanin dillancin labaran ƙasar ya ambato shugaban ƙasar yana cewa.

Shugaban ya jaddada cewa shi ya ga irin "jajircewa [ta dakarun] da kuma tasirinta,” yana mai yabawa da ayyukan dakarun operation Niya da kuma sadaukarwarsu.

 Shugaban ya kuma tabbatar wa dakarun cewa ƙasar baki ɗaya tana sane da ƙoƙarinsu.

“Domin ci-gaba da kuma samun nasarar kawo ƙarshen wannan rashin tsaron, gwamnati tana iya ƙoƙarinta, Muna sane da girman ƙasarmu da kuma ƙwarewar ko wane fagen daga,” in ji shugaban.

Shugaban ya ƙara da cewa abin da ya gani da idonsa ya ƙarfafa matakinsa na ƙara ɗaukar ƙarin jami’an tsaro domin iya cike dukkan yankin nan gaba.

 “Daukar jami’an ba shi ne kawai ba, dole mu ba su horo da kuma kayan aiki ta yadda za su iya tunkarar barazana. Idan ina maganar kayayyakin aikin wannan ya haɗa da na ƙasa da na sama,” in ji shugaban

Shugaban da ya samu tarbar malama da sarakunan  gargajiya da mutanen jihar Tilleberi, yana ziyara ne a yankin domin ƙarfafa wa dakarun da ke yankin da ke fama da matsalar hare-haren ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga.

Kamfanin dillancin labran ƙasar ta ruwaito cewa shugaban ƙasar ya fara ziyayar aiki a jihar Tilleberin ne tun ranar 4 ga watan Oktoba kuma ziyarar ta ci gaba ranar Lahadi 5 ga watan Oktoba.

Rumbun Labarai
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya