| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Ayyukan da sojojin Nijar suke yi a yankin Tillaberi sun fara tasiri: Shugaba Tiani
Shugaba Tiani ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ziyara Jihar Tilleberi inda ya yi rangadin dakarun da ke jihar wadda ke fama da matsalar tsaro.
Ayyukan da sojojin Nijar suke yi a yankin Tillaberi sun fara tasiri: Shugaba Tiani
Shugaban Nijar ya kai ziyarar aiki jihar Toilleberi da ke fama da hare-haren 'yan ta'adda
6 Oktoba 2025

Shugaban ƙasar Nijar Janar Abdourahamane Tiani ya shaida wa jami’an tsaron runduna ta 9 mai suna “Operation Niya,” cewa “ayyukan da kuke yi kullum sun fara tasiri.”

Shugaba Tiani ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ziyara Jihar Tilleberi inda ya yi rangadin dakarun da ke jihar wadda ke fama da matsalar tsaro.

Janar Abdourahamane Tiani ya taya dakarun tsaron murna game da gagaruman ƙoƙarin da suke yi a ko wace rana kan tabbatar da yanayi na tsaro domin amfanin dukkan al’umma.

 "Aikin da kuke yi a ko wace rana ya fara tasiri," kamar yadda kamfanin dillancin labaran ƙasar ya ambato shugaban ƙasar yana cewa.

Shugaban ya jaddada cewa shi ya ga irin "jajircewa [ta dakarun] da kuma tasirinta,” yana mai yabawa da ayyukan dakarun operation Niya da kuma sadaukarwarsu.

 Shugaban ya kuma tabbatar wa dakarun cewa ƙasar baki ɗaya tana sane da ƙoƙarinsu.

“Domin ci-gaba da kuma samun nasarar kawo ƙarshen wannan rashin tsaron, gwamnati tana iya ƙoƙarinta, Muna sane da girman ƙasarmu da kuma ƙwarewar ko wane fagen daga,” in ji shugaban.

Shugaban ya ƙara da cewa abin da ya gani da idonsa ya ƙarfafa matakinsa na ƙara ɗaukar ƙarin jami’an tsaro domin iya cike dukkan yankin nan gaba.

 “Daukar jami’an ba shi ne kawai ba, dole mu ba su horo da kuma kayan aiki ta yadda za su iya tunkarar barazana. Idan ina maganar kayayyakin aikin wannan ya haɗa da na ƙasa da na sama,” in ji shugaban

Shugaban da ya samu tarbar malama da sarakunan  gargajiya da mutanen jihar Tilleberi, yana ziyara ne a yankin domin ƙarfafa wa dakarun da ke yankin da ke fama da matsalar hare-haren ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga.

Kamfanin dillancin labran ƙasar ta ruwaito cewa shugaban ƙasar ya fara ziyayar aiki a jihar Tilleberin ne tun ranar 4 ga watan Oktoba kuma ziyarar ta ci gaba ranar Lahadi 5 ga watan Oktoba.

Rumbun Labarai
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata