| Hausa
SIYASA
3 minti karatu
Ministan Kudin Benin Romuald Wadagni ya lashe zaben shugaban kasar
Romuald Wadagni ya samu kashi 94 cikin 100 na ƙuri'un da aka kaɗa inda ya doke ɗan takarar jam'iyyar hamayya Paul Hounkpe, in ji sakamako na wucin-gadi.
Ministan Kudin Benin Romuald Wadagni ya lashe zaben shugaban kasar
Ɗantakaran shugaban ƙasa Romuald Wadagni na gaishe da magoya baya a wani gangami a Cotonou, Jamhuriyar Benin. / REUTERS
19 awanni baya

Ministan Kuɗin Benin ya yi nasara da gagarumin rinjaye a zaɓen shugaban ƙasa da aka yi ranar 12 ga watan Afrilu, inda ya samu fiye da kashi 94 cikin 100 na ƙuri’un da aka kaɗa, kamar yadda sakamako na wucin-gadi da hukumar zaɓen ƙasar ta fitar ranar Litinin ya nuna.

Shugaban hukumar zaɓe, Sacca Lafia, ya bayyana ta gidan talbijin na ƙasar cewa bayan ƙidaya fiye da kashi 90 cikin 100 na ƙuri’un da aka kaɗa, Romuald ‌Wadagni ya samu gagarumin rinjaye.

Lafia ya bayyana cewa Wadagni-Talata ya samu ƙuri’u 4,252,347 yayin da ɗan takarar hamayya Paul Hounkpe ya samu ƙuri’u 269,433, waɗanda daidai suke da kashi 5.95 cikin 100 na ƙuri’un da aka kaɗa.

Hukumar ta ce an haɗa sakamakon ne daga mazaɓu 15,814 daga cikin jumullar mazaɓu 17,463, wanda ya yi daidai da kashi 90.55 cikin 100 na mazaɓun gaba ɗaya.

Lissafin da ba za a iya sauyawa ba

Ta ƙara da cewa “giɓin da ke tsakanin ‘yantakaran ya kai yadda haɗa sauran sakamakon ba zai sauya matsayinsu ba, lamarin da ya sa ba za a iya sauya lissafin sakamakon ba.”

Fitowar masu ƙada ƙuri’u ya tsaya a kan kashi 58.75 cikin , inda masu ƙada ƙuri’u 4,640,354 suka ƙada ƙuri’u daga cikin mutum 7,897,287 da suka yi rajista.

Daga cikin waɗannan , ƙuri’u 4,522,756 ne aka tabbatar cewa suna da inganci, yayin da ƙuri’u 117,598 suka lalace.

Masu AlakaTRT Afrika - Ana gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Jamhuriyar Benin

Hukumar ta bayyana cewa an gudanar da zaɓen ne a faɗin ƙasar da kuma cibiyoyi 14 na ƙada ƙuri’u a ƙetare. Duk da rahotanni na ƙoƙarin katse harkar a wasu wurare a arewacin ƙasar, ta ce dakarun tsaro sun tabbatar da cewa ‘yan ƙasar sun iya zaɓe ba tare da wani tsaiko ba.

Hukumar ta kuma bayyana amfani da wata kafar dijital ta tura saƙonni wadda ta ce ta tabbatar da “iya ganowa ba tare da tsaiko ba da kuma tura bayanai na zaɓe.”

Kotun tsarin mulki

Za a tura sakamako na wucen gadi ga kotun tsarin mulki ba tare da ɓata lokaci ba, wadda ke da iko na ƙarshe wajen tabbatar da sahihaanci da kuma bayyana sakamakon zaɓen.

A ƙarƙashin tsarin zaɓen Benin, hukumar zaɓen ce ke da alhaƙin shiryawa da kuma bayyana sakamakon zaɓe na wucen gadi, yayin da kotun tsarin mulki ne ke da ikon yanke hukunci kan taƙaddama ta zaɓe da kuma tabbatar da sakamakon zaɓe na ƙarshe.

An gudanar da zaɓen ne ranar 12 ga watan Afrilu a faɗin ƙasar da kuma ƙetare.

Rumbun Labarai
Za a ci gaba da tsare El-Rufai yayin da kotu ta ɗage sauraron buƙatar neman beli zuwa 14 ga Afrilu
Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara a Nijeriya ya fice daga PDP zuwa APC
Jam’iyyun Adawa a Nijeriya sun yi watsi da Dokar Zabe ta 2026, sun nemi a yi sabon gyara
Jajircewar Turkiyya a Afirka: Labarin haɗin-kai da kyakkyawan fata
Martanin duniya a yayin da Isra’ila ke rajistar mallake Gabar Yammacin Kogin Jordan
Shugaban Nijar ya ziyarci Aljeriya, lamarin da ya nuna ƙarshen tsamin dangantaka tsakanin ƙasashen
Trump ya bar ƙofar Iran a bude, kuma Netanyahu ba zai iya rufe ta ba
Yadda 'yan Nijeriya suka fusata kan matakin Amurka na saka wa Kwankwaso takunkumi
Majalisar Dattijan Nijeriya ta amince da tsarin aika sakamakon zabe kai-tsaye ta intanet
Taƙaddama a kan gyaran dokar zaɓe ta Nijeriya
Ghana ta yi wa jakadanta a Nijeriya kiranye kan zargin maguɗin zaɓe
Iran ta ce ta shiga tattaunawar Oman da Amurka da 'kyakkyawar niyya'
Masar da Saudiyya sun yi kira ga samar da hanyoyin da suka dace kafin tattaunawar Amurka da Iran
Greenland ba hajar sayarwa ba ce
Yayin da duniya ta koma kasuwar buƙatar diflomasiyya, wai zai tsaya wa ƙasashe marasa ƙarfi a 2026?
Amurka ta dakatar da bai wa ‘yan Nijeriya biza
Alkawarin dala miliyan 150 zai sake gina Aleppo da yaƙi ya lalata
Yadda 'nadamar zalunci' ke janyo rushewar lafiyar ƙwaƙwalwa a rundunar sojin Isra’ila
Me ya sa Trump da masu sharhi da ke da ra’ayin rikau ke sa ido kan al’ummar Somalia da ke Minnesota?
Shugaban Nijar Tiani ya karɓi shugaban Bilma bayan ya yi watanni 16 a hannun masu garkuwa da mutane