| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
Fiye da mutane miliyan 45 a Nijeriya har yanzu suna yin bahaya a waje, kuma kusan kashi 25 cikin 100 na al'ummar ƙasar ne kawai suke da damar samun wurare masu tsafta da aka ware don bahaya, a cewar ministan muhalli na Nijeriya
'Yan Nijeriya miliyan 45 suna bahaya har yanzu a waje — Ministan Muhalli
'Yan Nijeriya miliyan 45 har yanzu suna yin bahaya a fili - Ministan Muhalli
20 Nuwamba 2025

Nijeriya na fuskantar matsalar tsaftar muhalli mai tsanani, inda fiye da 'yan ƙasar miliyan 45 ke ci gaba da yin bahaya a waje, in ji Ministan Muhalli na Nijeriya Mallam Balarabe Lawal.

Ministan ya bayyana haka ne a Abuja a yayin taron manema labarai kan bikin Ranar Banɗaki ta Duniya ta 2025, wanda aka yi wa take da "Tsabtace Muhalli a Duniyar da ke Canzawa" ƙarkashin maudu’in ‘‘Muna Buƙatar Bandaki a ƙullum.’’

Malam Lawal ya yi da yanayin da ake ciki a matsayin wata babbar matsala ta lafiyar al’umma da kuma ƙalubane na muhalli.

Ministan, wanda Sakataren Dindindin, Mallam Mahmud Kambari ya wakilta, ya ce kashi 25 cikin 100 na 'yan Nijeriya ne kawai suke da damar samun wurare masu tsafta da aka ware, don yin bahaya duk da ƙoƙarin da duniya ke yi na inganta tsaftar muhalli.

"A faɗin duniya, kimanin mutane biliyan 4.2 ba su da damar yin bahaya a wuraren da aka ware mai aminci.

“A Nijeriya kuwa, sama da mutane miliyan 45 har yanzu suna yin bahaya a fili, kuma kashi ɗaya cikin huɗu na al'ummar ƙasar ne kawai ke amfani da wurare tsaftacce da aka ware masu aminci," in ji shi.

Ministan ya koka kan yadda makarantu, da asibitoci, da cibiyoyin gwamnati da dama ba su da bandakuna kwata-kwata ko kuma suna amfani da waɗanda ba a kula da su sosai.

Ya kuma ƙara da cewa, har yanzu cibiyoyin birane da dama suna dogaro ne kan tsarin magudanar tattara shara wadanda suka gaza, lamarin da ke janyo kwararar ruwan datti zuwa cikin koguna da rafuka - yanayin da ke mummunan tasiri ga lafiyar dan’adam.

A cewar ministan, rashin tsaftar muhalli na ci gaba da haifar da barkewar cutar kwalara da gudawa da taifod da cututtukan da ke haifar da tsutsitsi cikin mutum da ke kashe dubban ‘yan Nijeriya kowace shekara, musamman yara 'yan ƙasa da shekara biyar.

Ya kuma yi gargaɗin cewa rashin tsaftar muhalli yana taimakawa wajen hana ƙwayoyin cuta mutuwa kuma yana haifar da cikas ga ci gaban Nijeriya na shirin SDG 6.2.

Rumbun Labarai
Jerin lokutan da aka shafe ana shari'ar Nnamdi Kanu, jagoran 'yan a-waren Biafra a Nijeriya
Yadda ta kaya a zaman 'yan majalisar Amurka kan zargin yi wa Kirisotci kisan kiyashi a Nijeriya
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai da ma’aikata a wata makaranta a Jihar Neja
Jagoran ƴan-awaren Biafra: Babbar Kotu a Nijeriya ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai
Ribadu ya jagoranci wata tawagar Nijeriya mai ƙarfi zuwa Amurka kan zargin kashe Kiristoci a ƙasar
Kotu ta yanke wa wani shugaban ISWAP da ya tsara hare-haren kano na 2012 ɗaurin shekara 20
Tinubu ya ɗaga tafiyarsa tarukan G20 da AU-EU saboda yanayin rashin tsaro da ake ciki a Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta nemi a ɗauki ƙarin sojoji 100,000 don magance rashin tsaro
Tinubu ya yi alhinin mutuwar Janar Uba da 'yan ta'adda suka kashe a Borno
Majalisar Dokokin Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis
Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi  a tsaurara neman 'yan matan da aka sace
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi
Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire
Rikicin PDP: Ɓangaren Wike ya yi watsi da kora yayin da jihohi huɗu ke ƙalubalantar Makinde
‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi
Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja
Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya - Gwamna Abba Kabir
Yaya karawar Nijeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo za ta kasance?