AFIRKA
2 minti karatu
An jinkirta buɗe makarantu a Nijar zuwa 15 ga Oktoba sakamakon ruwan sama
Hukumomi a Nijar sun bayyana cewa jinkirta buɗe makarantu a ƙasar ya zama dole saboda yanayin damina mai tsawo da kuma ambaliya, lamarin da ya sanya makarantu ba sa aiki kana ajujuwa da dama sun cika da ruwa.
An jinkirta buɗe makarantu a Nijar zuwa 15 ga Oktoba sakamakon ruwan sama
Gwamnatin Nijar ta jinkirta lokacin bude makaratu a kasar daga 1 ga Okatoba zuwa 15 ga watan saboda ruwan sama
30 Satumba 2025

Cikin shekaru biyu a jere, tsarin kalandar karatu a Nijar ya fuskanci tsaiko sakamakon ruwan sama mai ƙarfi da kuma ambaliya da suka tilasta wa gwamnati jinkirta buɗe makarantu a faɗin ƙasar.

A wata sanarwa da ofishin babban sakataren gwamnatin ƙasar ya fitar a ranar Litinin, ya bayyana cewa an jinkirta shekarar karatu ta 2025-2026 da mako biyu, wato daga ranar 1 ga Oktoba zuwa 15 ga watan Oktoba, kamar yadda jaridar Actu Niger ta rawaito.

Sanarwar wadda babban sakataren Mahamane Roufal Laouali ya sanya wa hannu, ta ce matakin ya shafi ɗalibai kusan miliyan uku a faɗin ƙasar.

Hukumomi a ƙasar sun bayyana cewa, ɗage lokacin buɗe makarantu a Nijar ya zama dole saboda yanayin damina mai tsawo da aka samu, lamarin da ya sanya makarantu ba sa aiki kuma ajujuwa da dama sun cika da ruwa ko kuma suna buƙatar gyara cikin gaggawa.

An umarci gwamanoni da hakimai da jami’an ilimi su haɗa kai domin gyara makarantun gabanin sabuwar ranar da aka sanya ta buɗe makarantu a faɗin ƙasar.

Wannan dai ba shi ne karo na farko da yanayin damina ke kawo cikas ga tsarin kalandar karatu a Nijar ba. A shekarar 2024, sai da ambaliyar ruwa ta tilasta wa hukumomi jinkirta soma shekarar karatu daga 2 ga watan Oktoba zuwa 28 ga Oktoba.

Hakan ya biyo bayan lalacewar makaratu da dama ko kuma mayar da su wuraren samun mafaka ga iyalai da suka rasa matsugunansu.

Kazalika ɗage lokacin buɗe makarantun ya daɗa ƙara matsin da tsarin ilimin Nijar ke ciki a ƙasar, inda a bana ake sa ran samun ɗalibai kusan miliyan uku.

Adadin ɗaliban dai ya nuna matsalolin da ake fuskanta kamar rashin isassun ajujuwa, da cunkoso a makarantu da kuma ƙarancin malamai.

Rumbun Labarai
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya