| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
3 minti karatu
Mafi yawan Amurkawa ba sa goyon bayan yaƙin Amurka kan Iran: Ƙuri'ar jin ra'ayi
Wani sabon jin ra’ayin jama’a da aka gdanar ya nuna kashi 54 na Amurkawa da suka amsa tambayoyi sun nuna rashin amincewa da yadda Trump ke tafiyar da yaki kan Iran.
Mafi yawan Amurkawa ba sa goyon bayan yaƙin Amurka kan Iran: Ƙuri'ar jin ra'ayi
Bayan kai harin Amurka-Isra'ila kan jajo ofis din 'yan sanda a Tehran. / Reuters
5 Maris 2026

Yawancin masu kada ƙuri'a a Amurka da suka yi rijista ba su amince da yadda Shugaba Donald Trump ke tafiyar da rikicin da ke tsakaninsa da Iran ba, kuma suna ganin bai kamata kasar ta fara kai hare-haren soji ba, a cewar wata sabuwar ƙuri'ar jin ra'ayin jama'a na NBC News.

Binciken ya gano kashi 54 cikin 100 na masu kada kuri'a ba su amince da manufar Trump game da Iran ba, yayin da kashi 41 cikin 100 suka amince. Wasu kashi 5 cikin 100 kuma ba su yanke shawara ko kuma ba su da ra'ayi.

Dangane da batun daukar matakin soji, kashi 52 cikin 100 sun ce bai kamata Amurka ta kai hari kan Iran ba, idan aka kwatanta da kashi 41 cikin 100 na wadanda suka goyi bayan shawarar. Kashi bakwai cikin 100 sun kasance ba su da tabbas.

Ra'ayoyi galibi suna bin bangaren jam'iyya, kodayake kuri'ar ta nuna karamin kaso amma mai muhimmanci na 'yan Republican ba su gamsu da shiga tsakani na soji ba.

Bambance-bambancen masu shekaru mabambanta su ma a bayyane suke, inda matasa da tsofaffi masu jefa kuri'a suka mayar da martani daban-daban a farkon yakin.

Sakamakon ya nuna yadda Amurkawa ke mayar da martani ga wani babban hari na soja da wani shugaban Amurka ya fara a lokacin yakin neman zabensa na 2024 na komawa Fadar White House kan yaƙe-yaƙe na ƙasashen waje.

A tarihi, binciken NBC News ya nuna cewa goyon bayan jama'a na farko ga tsoma bakin sojojin Amurka galibi yana da yawa.

Bincike daga farkon 2002 zuwa farkon 2003 ya nuna cewa yawancin Amurkawa sun goyi bayan matakin soja na kawar da Saddam Hussein daga mulki a Iraki.

Hakazalika, a watan Oktoba na 2001, kashi 87 cikin 100 na Amurkawa sun amince da yadda Shugaba George W. Bush ya tafiyar da "Yaƙin Ta'addanci" a lokacin harin farko da Amurka ta kai a Afghanistan bayan harin ta'addanci na 9/11.

Duk da haka, goyon bayan waɗannan yaƙe-yaƙe daga baya ya ragu, inda mafi rinjaye suka kammala da cewa yaƙe-yaƙen ba su kai darajar rayukan da aka kashe ba.

‘Yan jam’iyyar Republican na goyon baya yaƙar Iran

Goyon bayan da ake bayarwa kan kaiwa Iran hari ya fi karfi a tsakanin 'yan Republican.

Kashi 77 cikin 100 na masu kada kuri'a na jam'iyyar Republican sun ce Amurka ta yi daidai da ta kai hari, yayin da kashi 15 cikin 100 ba su yarda ba.

Binciken ya kuma nuna rarrabuwar kawuna a cikin jam'iyyar.

Daga cikin 'yan Republican da ke goyon bayan yunkurin Trump na Make America Great Again (MAGA), kashi 90 cikin 100 sun goyi bayan hare-haren, kashi 5 cikin 100 kuma sun nuna adawa da shi.

Daga cikin 'yan Republican da ke wajen reshen MAGA, kashi 54 cikin 100 sun goyi bayan matakin, yayin da kashi 36 cikin 100 suka nuna adawa da shi.

 

Rumbun Labarai
A shirye Iran take ta yi arangama da dakarun ƙasa na Amurka: babban jami'in diflomasiyya
Ankara na da ‘yancin mayar da martani don kare Turkiyya daga yaƙin Amurka-Isra'ila da Iran
Iran ta ce ta kai wa jirgin ruwan dakon mai na Amurka hari a Gulf
Iran ta yi iƙirarin kashe sojojin Amurka 500 a cikin kwanaki biyar na yaƙi
Shin yaƙin Amurka da Isra’ila a Iran duk dabara ce ta sake mamayar yankin Gabas ta Tsakiya?
'An gaya wa dakarun Amurka cewa yaƙin Iran ‘ƙudirar Ubangiji’ ce don kawo ƙarshen duniya'
Amurka ta yi asarar kayayyakin sojin na kusan $2bn a kwanaki 4 na yaƙi da Iran
Iran ta ce babu zancen tattaunawa da Amurka, ta sha alwashin kare kanta kawai
Ministan Turkiyya Fidan na yin tuntubar diflomasiyya a tsaka da hare-haren Amurka da Isra’ila a Iran
Yaƙin Iran da Isra'ila ya sa tafiya Umara zuwa Saudiyya na fuskantar barazana
Iran ta ce ta kai hari a wurare aƙalla 500 na Isra'ila da Amurka
Ƙasashen Afirka sun yunƙura don kare jama'arsu da ke  Gabas ta Tsakiya
Me ya rage wa Iran bayan Khamenei?
Jiragen yaƙin Amurka da dama sun faɗi a Kuwait, in ji ma'aikatar tsaron Kuwait
Iran ta harba makamai masu linzami Isra'ila, 9 sun mutu a Beit Shemesh, 12 sun mutu a faɗin ƙasar
Iran ta kafa majalisar jagorancin wucin-gadi a Iran bayan kashe Khamenei
Nijeriya, Senegal da Libya sun buƙaci a tsagaita wuta yayin da Isra'ila-Amurka ke rikici da Iran
Iraniyawa suna zanga-zanga bayan Amurka da Isra'ila sun kashe Khamenei
Iran ta tabbatar da kisan Ali Khamenei da iyalansa
Iran ta musanta iƙirarin Amurka da Isra'ila na kashe Jagoran Addini Ali Khamenei