| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Harin RSF a wani asibiti a Sudan ya kashe mutum 22, ciki har da ma'aikatan jinya
Ƙungiyar likitocin Sudan ta zargi dakarun RSF da aikata laifin yaƙi bayan kai harin bam a asibitin soji na Al-Kuweik.
Harin RSF a wani asibiti a Sudan ya kashe mutum 22, ciki har da ma'aikatan jinya
Ƙungiyar likitocin ta yi Allaha wadai da harin, tana mai cewa kai hari kan cibiyar jinya da kuma ma’aikatan jinya “laifin yaƙi ne" / Reuters
6 Fabrairu 2026

An kashe aƙalla mutum 22, ciki har da ma’aikatan jinya huɗu, yayin da wasu takwas suka jikkata bayan rundunar RSF ta kai harin bam a asibitin soji na Al-Kuweik a jihar Kudancin Kordofan ta Sudan, kamar yadda wata ƙungiyar ma’aikatan jinya ta bayyana.

A wata sanarwa da ta fitar ranar Alhamis, ƙungiyar likitocin Sudan ta ce waɗanda lamarin ya rutsa da su sun haɗa da daraktan asibitin da kuma wasu ma’aikatan jinya uku.

Ƙungiyar ta yi Allaha wadai da harin, tana mai cewa kai hari kan cibiyar jinya da kuma ma’aikatan jinya “laifin yaƙi ne da kuma tsagwaron keta dokokin ƙasa da ƙasa da suka tabbatar da kare fararen-hula da wuraren jinya.”

Ta ce harin wani ɓangare na jerin hare-hare a faɗin jihar Kudancin Kordofan ya tilasta dakatar da ayyuka a wasu asibitoci, lamarin da ya ta’azzara matsalar jinƙai tare da barazana ga abin da ya saura cikin harkar jinya ga fararen-hula.

Masu AlakaTRT Afrika - Sudan ta sake buɗe filin jiragen sama na Khartoum bayan yaƙin kusan shekaru uku

Ƙungiyar ta ɗoura wa RSF alhakin harin gaɓa ɗaya. Sannan ta yi kira ga ƙasashen duniya da hukumomin Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) da kuma ƙungiyoyin kare haƙƙin bil’adama su ɗauki mataki nan-take domin kawo ƙarshen hare-hare kan wuraren jinya.

Babu tsokaci nan-take daga RSF game da zargin.

Daga cikin jihohin Sudan18, rundunar RSF tana iko da dukkan jihohi biyar a yankin Yammacin Darfur, face wasu ɓangarori na Arewacin Darfur da kawo yanzu yake ƙarƙashin ikon soji.

Sojin na da iko a yawancin jihohi 13 a faɗin kudanci da arewaci da gabashi da kuma tsakiyar ƙasar, ciki har da babban birnin ƙasar, Khartoum.

Rikicin tsakanin sojin Sudan da ku ma rundunar RSF, wanda ya ɓarke a watan Afrilun 2023, ya kashe dubban mutane tare da raba miliyoyi da gidajensu.

Rumbun Labarai
Dalilin da ya sa Kenya da Ethiopia suka zama manyan masana'antun furanni a duniya
Ambaliyar ruwa ta kashe mutane 15 a Angola
Senegal ta haramta wa jami'an gwamnati tafiye-tafiye marasa muhimmanci zuwa ƙasashen waje
Yadda aikin dala miliyan 240 ke bai wa al’umar gaɓar teku a Benin da Mauritania damar gwagwarmaya
Gwamnatin Madagascar ta daƙile yunƙurin kashe shugaban ƙasar Michael Randrianirina
Sudan ta yi Allah wadai da 'mummunan' harin da RSF ta kai wani asibiti yayin allurar rigakafin yara
Ghana za ta fara aiwatar da shirin shiga ƙasar ba tare da biza ba ga dukkan 'yan Afirka
Shugaban riƙon jihar Kudu maso yammacin Somaliya zai hau kan mulki bayan ajiye aikin shugaba
Sudan ta nemi 'yan ƙasar da suka yi ƙaura zuwa ƙasashen waje saboda yaƙi su koma gida
Hukumar leƙen asirin Somalia ta kashe masu haɗa bama-baman Al Shabab
Mali ta musanta rahoton sakin ’yanta’adda 200 domin samun man fetur
An kasa cim ma matsaya kan sabbin sauye-sauye a tattaunawar WTO a Kamaru
Darasin da Togo ke koya wa sauran kasashe wajen magance cututtukan da aka yi watsi da su
’Yanbindiga sun kashe fararen-hula 16 kusa da iyakar Nijar da Mali
Nijar ta ƙaddamar da sabon katin ɗan ƙasa na zamani mai tambarin AES
Laifi mafi muni: AU ta nemi MƊD ta ɗauki mataki kan biyan diyyar cinikin bayi bayan MƊD ta tabbatar
Ghana ta sake yin bita kan tsarin yaƙi da ta’addanci sakamakon barazanar masu tsattsauran ra’ayi
Rasha ta yi iƙirarin cewa 'yan kwangilar sojin Faransa na da yawa a Afirka
Hukumomi a Nijar sun kama wani mutum a Zinder bisa zargin yawan kai wa 'mata' hari a kan babur
Me ya sa diyyar cinikin bayi da mulkin mallaka suka zama masu muhimmanci ga Afirka a 2026