| Hausa
TURKIYYA
2 minti karatu
Turkiyya ta yi gargaɗi kan tsoma baki daga waje a Iran, ta buƙaci a magance rikicin a cikin gida
Kakakin Jam’iyyar AK mai mulki a Turkiyya Omer Celik ya jaddada cewa tsoma baki, musamman wanda Isra’ila take rura wutarsa, na iya jawo babban rikici da rashin zaman lafiya mai zurfi a Gabas ta Tsakiya.
Turkiyya ta yi gargaɗi kan tsoma baki daga waje a Iran, ta buƙaci a magance rikicin a cikin gida
"Ba ma bukatar ganin afkuwar duk wani irin rikici a makociyarmu Iran,” in ji Celik / AA / AA
13 Janairu 2026

Turkiyya ta yi gargaɗin cewa duk wani tsoma baki na ƙasashen waje a maƙwabciyarta Iran zai ta'azzara rikice-rikice a ƙasashen biyu da kuma yankin Gabas Ta Tsakiya baki ɗaya, tana mai jaddada cewa ya kamata a warware matsalolin cikin gida na Iran ta hanyar tattaunawa da kuma yanayin zamantakewa na ƙasar.

Mataimakin Shugaban Jam'iyyar AK kuma Kakakin Jam'iyyar Omer Celik ya bayyana a ranar Litinin cewa Ankara ba ta son ganin rikici a Iran, duk da cewa ta amince cewa akwai matsaloli a cikin al'ummar Iran da ma a cibiyoyin gwamnati.

"Ba ma son wani rikici ya ɓarke ​​a maƙwabciyarmu Iran," Celik ya faɗa a wani taron manema labarai a hedkwatar jam'iyyar da ke Ankara bayan taron da shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya jagoranta.

Masu AlakaTRT Afrika - An kashe ɗansanda a kusa da Tehran yayin da zanga-zanga kan matsin rayuwa ta mamaye ƙasar Iran

Ya ce, kamar yadda shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya faɗa, ya kamata a warware matsalolin Iran ta hanyar yanayin cikin gida na al'ummar Iran da kuma aniyar ƙasa ta ƙasar.

Ƙaruwar rikici

"Shiga tsakani na ƙasashen waje zai haifar da mummunan sakamako," in ji Celik, yana mai ƙarawa da cewa musamman tsoma bakin da Isra'ila ke azalzalowa zai iya haifar da manyan rikice-rikice da rashin kwanciyar hankali a yankin.

Da yake jaddada cewa ya kamata a magance matsalar ta hanyar tattaunawa, sulhu da kuma ƙara tuntubar juna, Celik ya ce kalaman da jami'an Isra'ila suka yi kwanan nan game da Iran na iya haifar da rura wutar rikicin yankin.

"Wannan bakar hanyar za ta haifar da tashin hankali a duk faɗin yankin kuma dole ne a yi watsi da ita gaba ɗaya," in ji shi.

A halin yanzu Iran na fuskantar zanga-zanga mafi girma tun 2022, yayin da shugaban Amurka Donald Trump ya ce Washington za ta iya shiga tsakani idan aka yi amfani da ƙarfi a kan masu zanga-zanga, wanda hakan ke ƙara nuna damuwa game da tabarbarewar rikicin.

Rumbun Labarai
Adadin jama'ar Turkiyya ya kai miliyan 86 a 2025 yayin da jama'ar ƙasar ke ƙara yawa
Matar Shugaban Turkiyya da Sarauniyar Jordan sun ƙara jaddada ƙawance a Istanbul
Turkiyya ta kama jami'an Mossad na Isra'ila biyu a Istanbul kan leƙen asiri
Shugaba Erdogan ya tuna da girgizar ƙasa, ya ce ‘Turkiyya ta cika alkawarinta‘ na sake gina gidaje
Turkiyya ta bunƙasa taimakon da ta ke ba Somaliya na sojojin sama da ƙasa don yaƙi da ta'addanci
Shugaban Turkiyya Erdogan ya gana da Yarima Mai Jiran Gado na Saudiyya Mohammed bin Salman a Riyadh
Shugaban Turkiyya zai ziyarci Saudiyya da Masar a cikin wannan makon
Fidan na Turkiyya ya gargaɗi Amurka kan kai wa Iran hari, ya ce Tehran a shirye take ta tattauna
Zaman lafiyar Iran na da muhimmanci ga tsaron yankin: Turkiyya
Turkiyya da Nijeriya sun ƙudiri aniyar kyautata alaƙar kasuwanci, zuba jari da tsaro
Erdogan da Trump sun tattauna kan Syria da Kwamitin Zaman Lafiya na Gaza
Turkiyya ta goyi bayan Nijeriya a yaƙi da ta'addanci yayin da Erdogan ya karbi baƙuncin Tinubu
Ziyarar Tinubu a Turkiyya: Muhimman abubuwa a tsarin dangatakar Nijeriya
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Fidan ya gana da takwaransa na Nijeriya Tuggar
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya da takwaransa na Nijeriya za su gana kan cinikayya da tsaro
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hidan ya yaba da "Kwamitin Zaman Lafiya" na Gaza
Turkiyya ta ɗauki dukkan yarjejeniyar zaman lafiyar Gaza da mahimmanci: Erdogan
Fidan na Turkiyya zai halarci bikin sa hannu na 'Hukumar Zaman Lafiya' ta Gaza a Switzerland
An tono makarantar Islamiyya mai shekara 900 yayin aikin sabunta birni a yankin Anatolia a Turkiyya
‘Syria ta ‘yan Syria ce’: Erdogan ya yaba da yarjejeniyar zaman lafiya ta Damascus