| Hausa
TURKIYYA
2 minti karatu
Turkiyya ta yi kira ga Tunisia da ta saki jagoran Ennahda Ghannouchi da ke tsare a kurkuku
Kakakin Majalisar Dokoki Numan Kurtulmus ya ce damuwar shekaru da lafiyar Rached Ghannouchi na bukatar kulawar likita da yanayin tausayawa.
Turkiyya ta yi kira ga Tunisia da ta saki jagoran Ennahda Ghannouchi da ke tsare a kurkuku
"Idan aka yi la'akari da tsufansa da yanayin lafiyarsa, bai kamata a yi watsi da muhimmancin halin da Ghannouchi ke ciki ba," in ji Kurtulmus.

Shugaban Majalisar Dokokin Turkiyya Numan Kurtulmus a ranar Alhamis ya yi kira da a saki shugaban ƙungiyar Ennahda da ke tsare kuma tsohon shugaban Majalisar Dokokin Tunisia Rached Ghannouchi tare da ba shi cikakkiyar kulawar lafiya.

Kurtulmus ya bayyana a shafin sada zumunta na NSosyal na Turkiyya cewa yana bin diddigin abubuwan da ke faruwa game da Ghannouchi, wanda ya bayyana a matsayin "ɗaya daga cikin manyan mutane masu fafutukar zaman lafiya da dimokuraɗiyya da haɗin kai."

Ya ce Ghannouchi ya kawo ƙarshen yajin cin abinci da magunguna bisa buƙatar tawagar likitoci da ke sa ido kan yanayin lafiyarsa.

"Idan aka yi la'akari da tsufansa da matsalolin lafiyarsa, bai kamata a yi watsi da muhimmancin halin da Ghannouchi ke ciki ba," in ji Kurtulmus.

Ya bayyana Ghannouchi a matsayin wanda ya sadaukar da rayuwarsa ga "makomar al'ummar Tunisia, 'yanci, adalci da dimokuraɗiyya," yana mai cewa bai yi watsi da "ƙa'idojin da ya yi imani da su da gwagwarmayar dimokuraɗiyya ba" duk da matsin lamba da kuma ɗaurin kurkuku.

Kurtulmus ya ce Ghannouchi ya sami karɓuwa sosai a Tunisia da kuma ƙasashen duniya ta hanyar "matsayinsa na kare dimokuraɗiyya a lokacin sauyi, ƙarfin iliminsa da ra'ayoyinsa."

"A matsayin wani misali na irin kyakkyawar alaƙar 'yan'uwa tsakanin al'ummar Turkiyya da Tunisia, ina yi masa fatan alheri da kuma fatan ya dawo da lafiyarsa da wuri-wuri," in ji shi.

"Babban fatanmu shi ne ya sami cikakkiyar kulawar likita, ya sami cikakkiyar kulawa da ta dace da mutuncin ɗan adam, sannan a sake shi."

Tsare Ghannouchi

An ɗaure Ghannouchi, tsohon kakakin majalisar da Shugaba Kais Saied ya rusa, tun bayan kama shi a ranar 17 ga Afrilun 2023.

Kotu ta ba da umarnin a tsare shi a wata shari'a da ta shafi kalaman da aka danganta shi da su, bisa zargin "tunzura jama’a su yi wa jami'an tsaro tawaye." Daga baya an yanke masa hukuncin ɗaurin kurkuku a shari'o'i da dama amma ya yi watsi da tuhumar da ake masa d acewa siyasa ce kawai.