| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Sabbin takunkuman da Amurka ta saka mana ta'addanci ne a fannin tattalin arziki, in ji Iran
A cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta fitar a ranar Alhamis, ta bayyana takunkuman a matsayin “ci gaba da nuna gaba da ƙiyayya na tsawon shekaru 73 da ’yan siyasar Amurka suke nuna wa al’ummar Iran.”
Sabbin takunkuman da Amurka ta saka mana ta'addanci ne a fannin tattalin arziki, in ji Iran
Sanarwar ta ƙara da cewa Iran na ci gaba da tsayuwa “tsayin daka tare da ƙuduri” wajen kare muradunta na ƙasa daga matsin lambar soja / Reuters

Tehran ta yi Allah wadai da wani sabon jerin takunkuman tattalin arziki da kasuwanci da Amurka ta kakaba wa Iran, tana mai bayyana su a matsayin “ta’addanci kan tattalin arziki.”

A cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta fitar a ranar Alhamis, ta bayyana takunkuman a matsayin “ci gaba da nuna gaba da ƙiyayya na tsawon shekaru 73 da ’yan siyasar Amurka suke nuna wa al’ummar Iran.”

“Takunkuman tattalin arziki da Amurka ta kakaba wa Iran, waɗanda suka shafi muhimman haƙƙoƙin ɗan’adam na Iraniyawa, sun zama ta’addancin tattalin arziki da kuma laifi kan bil’adama,” in ji ma’aikatar.

Ta ƙara da cewa waɗanda ke tsarawa da aiwatar da irin waɗannan matakai “sun cancanci a gurfanar da su a gaban shari’a tare da hukunta su saboda aikata irin waɗannan munanan laifuka.”

‘Haramtattun buƙatu na rashin mutunci’

A cewar ma’aikatar, sabbin takunkuman sun zo ne bayan abin da ta bayyana a matsayin “yaƙin haɗin gwiwa na Amurkawa da Yahudawa masu tsaurin ra’ayi” kan Iran, da kuma gazawar Washington daga baya wajen tilasta wa al’ummar Iran miƙa wuya ga “buƙatu marasa halacci da rashin mutunci.”

Masu AlakaTRT Afrika - Iran na duba yiwuwar kai hari kan cibiyoyin sojin Amurka da ke Turai: Rahoto

Ta kuma bayyana matsin tattalin arzikin da Amurka ke yi a matsayin “ɗaya daga cikin fuskokin yaƙi,” tana mai cewa dogaro da Washington kan dabarun biyu na haifar da barazana ga zaman lafiya da tsaron duniya.

Sanarwar ta ƙara da cewa Iran na ci gaba da tsayuwa “tsayin daka tare da ƙuduri” wajen kare muradunta na ƙasa daga matsin lambar soja, tattalin arziki, siyasa da kuma ta fannin tunani daga Amurka.

A ranar Laraba, Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da shirinsa na ƙaddamar da abin da ya kira “mafi tsananin matakin tattalin arziki da aka taɓa ɗauka kan kowace ƙasa,” yana mai bayyana yaƙinsa na matsin lamba kan Iran a matsayin “Yaƙin Tattalin Arziki da Mayar da Ƙasa Saniyar-Ware a Duniya a matakin da ba a taɓa gani ba.”

Ya sha alwashin katse hanyoyin kuɗi da ke tallafa wa Tehran, yana mai gargaɗin cewa ƙasashen da ke samar wa Iran da wata “hanyar tsira ta tattalin arziki” — ta hanyar cibiyoyin kuɗinsu, kamfanoni, filayen jiragen sama ko hukumomin gwamnati — za su fuskanci mummunan sakamako na tattalin arziki.