| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Dakarun Nijeriya sun kashe 'yanta'adda tare da ƙwace makamai a Jihar Filato
Duk da kafiyarsu daga farko, ƙarfin makaman sojojin ya rinjayi ‘yanta’addan daga baya inda aka kashe 10 daga cikinsu yayin da wasu suka tsere cikin dazukan da ke kusa, in ji sanarwar.
Dakarun Nijeriya sun kashe 'yanta'adda tare da ƙwace makamai a Jihar Filato
Sojin Nijeriya na yaƙar ta'addanci a sassan Nijeriya ciki har da cihar filato dake tsakiyar ƙasar / AFP
10 Afrilu 2026

Dakaru na musamman na rundunar Operation Enduring Peace da ke aikin wanzar da tsaro a jihar Filato da ke tsakiyar ƙasar da ‘yan sa-kai sun yi nasarar kashe ‘yanta’adda goma a wani aikin kakkaɓe masu aikata laifuka da suka yi a ƙauyukan Daba da Seri da ke ƙananan hukumomin Wase da Kanam.

​Wata sanarwa da jami’in watsa labarai na rundunar, Kyafin Chinonso Polycarp Oteh, ya fitar ranar Jumma’a ta ce dakarun rundunar sun ƙaddamar da aikin ne da safiyar ranar Alhamis 9 ga watan Afrilun shekarar 2026 inda suka toshe wasu hanyoyi masu muhimmanci tsakanin Dutesen Zaki da Dajin Odare.

“Yayin aikin, an ga gungun ‘yanta’adda bisa babura inda suke tafiya a wata sananniyar hanyar daji, kuma nan-take dakarun suka yi arangama da masu aikata laifukan inda suka rinjaye su da ƙarfin makamansu,” in ji sanarwar.


Duk da kafiyarsu daga farko, ƙarfin makaman sojojin Nijeriya ya rinjayi na ‘yanta’addan daga baya inda aka kashe 10 daga cikinsu yayin da wasu suka tsere cikin dazukan da ke kusa, in ji sanarwar.

A wani batu makamancin hakan, bayan wani rahoto na wani hari kan matafiya a kan hanya a Razat da Kafi Abu, dakarun Nijeriya sun ƙaddamar da hari na gaggawa kan masu aikata laifuka.

Fara arangamar ke da wuya sai masu aika-aikar suka janye zuwa dazukan da ke kusa inda jami’an tsaro suka bi su nan-take domin tabbatar da zaman lafiya a yankin.

​Sanarwar ta ƙara da cewa dakarun sun ƙaddamar da bincike a ƙauyukan Suma Suga da Takwok , da kuma wuri mai tsaunuka da ke kusa da su.

Wannan ya sa dakarun sun gano kayayyakin da masu aikata laifukan suka bari a baya ciki har da bindigogi ƙirar AK-47 guda uku da harsasai da sauransu.

Rumbun Labarai
Rundunar Sojin Nijeriya ta ce an kashe dakarunta a harin da Boko Haram ta kai hedkwatarsu a Borno
‘Gwarazan da ba za a iya mantawa da su ba’, Tinubu na juyayin kisan sojojin Nijeriya a harin Borno
Amurka ta bai wa jami'anta umarnin barin ofishin jakadancinta a Nijeriya saboda rashin tsaro a ƙasar
Aƙalla mutum 60 aka kashe a hare-hare daban-daban a arewa maso yammacin Nijeriya cikin mako guda
Bankin Duniya ya ce tattalin arzikin Nijeriya zai habaka a 2026
An mayar da 'yan Nijeriya 179 gida daga Libya
Babbar kotun Nijeriya ta ɗaure 'yanta'adda biyar
Dakarun Nijeriya sun kashe 'yanta'adda biyar, sun kama wanda ake zargi da garkuwa da mutane a Filato
Matatar Dangote ta ƙara man da take turawa ƙasashen Afirka yayin da yaƙin Iran ya katse jigilar mai
An buƙaci Nijeriya ta gyara yadda ake bayar da labaran rikice-rikice
An kama mutum biyar kan harbin bindiga ba bisa ƙa’ida ba da 'ya kashe' yarinya Maiduguri a Nijeriya
Abin da ya sa Kano Pillars ta lallasa Bendel Insurance da ci 4-0 — Koci
Dakarun Nijeriya sun kashe 'yanta'adda yaran Ado Aleiro
‘Yanta’adda sun kai hari ofishin ‘yansanda a Borno, sun kashe jami’ai huɗu
Rundunar Sojin Nijeriya ta amince a tura ƙarin sojoji 850 zuwa Filato saboda matsalar tsaro
Dalilin da ya sa Shugaba Tinubu ya gana da waɗanda harin Filato ya shafa a filin jirgin sama
A karon farko Nijeriya ta fitar da ganga 950,000 ta ɗanyen mai samfurin Cawthorne zuwa Indiya
Jam'iyyar ADC ta zargi gwamnatin Nijeriya kan matakin INEC na cire David Mark daga shugabancinta
Nijeriya za ta bayar da ƙarin ɗanyen mai ga matatar man Dangote a watan Mayu
Shugaban Nijeriya Tinubu na neman sake aro dala biliyan 6 daga UAE da Birtaniya