| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
An yanke wa Sojojin Nijeriya uku hukuncin ɗaurin rai da rai
An yanke wa sojojin hukuncin laifuka da dama, wadanda suka hada da sata, da yin mu’amala da harsasai ba bisa ƙa’ida ba, da kuma taimaka wa ‘yan ta’adda wadanda duk hukuncinsu ke karkashin dokar kotun sojin Nijeriya
An yanke wa Sojojin Nijeriya uku hukuncin ɗaurin rai da rai
An yanke wa Sojojin Nijeriya uku hukuncin ɗaurin rai da rai bisa laifin sayar da makamai ga 'yan ta'adda
25 Satumba 2025

Wata kotun sojin a Nijeriya ta musamman da ke zamanta a birnin Maiduguri na jihar Borno a Nijeriya ta yanke hukuncin ɗaurin-rai-da-rai ga wasu sojoji uku da kuma wani soji ɗaya da zaman gidan yari na tsawon shekaru 15 bisa samun su da laifin sayar da makamai ba bisa ka'ida ba ga ƙungiyoyin 'yan ta'adda.

An yanke wa sojojin hukuncin laifuka da dama, wadanda suka hada da sata, da yin mu’amala da harsasai ba bisa ƙa’ida ba, da kuma taimaka wa ‘yan ta’adda wadanda duk hukuncinsu ke karkashin dokar kotun.

Birgediya Janar Ugochukwu Unachukwu, mukaddashin kwamandan runduna ta 7 kuma kwamandan sashi 1, na Operation Hadin Kai (OPHK) ne ya jagoranci shari’ar ta kama mutanen da suka hadar da Raphael Ameh da Sergent Ejiga Musa da kuma Lance Corporal Patric Ocheje da laifin cinikayyar makamai da alburusai tsakaninsu da mayaƙan Boko Haram.

Kazalika kotun ta sami Omitoye Rufus mai rike da muƙamin Corporal da laifin haɗa baki wajen aikata wannan laifi, inda shi kuma aka yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru 15 a gidan yari.

The court ruled that their actions posed a direct threat to military operations and national security, constituting a clear case of aiding the enemy.

Kotun ta ce laifukan da suka aikata na barazana kai tsaye ga ayyukan soji da kuma tsaron ƙasa, wanda kuma a bayyane yake cewa hakan na taimaka wa maƙiya.

Rumbun Labarai
Rundunar sojin Nijeriya ta kuɓutar da masu yi wa ƙasa hidima 47 daga 'yan Boko Haram a Borno
Nijeriya ta dakatar da aiwatar da harajin kashi 15% kan shigar da fetur da dizal cikin ƙasar
'Musulmai ne Boko Haram ta fara yi wa ɓarna': AU ta yi watsi da Trump kan kisan kiyashi a Nijeriya
Za mu bai wa kowane jami'in soja da ke bakin aikinsa kariya  - Ministan Tsaron Nijeriya
An kama hodar ibilis mai nauyin kilogiram 1,000 a Nijeriya
‘Yan wasan Super Eagles sun ƙaurace wa atisaye kan rashin biyansu alawus
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya