GABAS TA TSAKIYA
1 minti karatu
Sojojin Isra'ila sun fara janyewa a hankali zuwa gabashin Gaza: Kafofin watsa labarai
Kafar Channels 12 ta Istara'ila ta ce ana sa ran sojojin za su janye zuwa gabashi daga Rafah da Khan Younis, sannan daga yankunan arewacin Gaza inda za su nufi iyakar Isra'ila.
Sojojin Isra'ila sun fara janyewa a hankali zuwa gabashin Gaza: Kafofin watsa labarai
Motar sojojin Isra'ila tana tafiya a wani titin Gaza.
10 Oktoba 2025

Rundunar sojan Isra'ila ta fara janye sojojinta daga Gaza zuwa wuraren da aka ƙayyade a cikin shirin Shugaban Amurka Donald Trump na kawo karshen yaiƙn da ake yi a yankin na Falasdinawa da aka killace, kamar yadda kafofin watsa labarai na Isra'ila suka ruwaito.

“A cikin sa'o'i 24 masu zuwa, sojojin Isra'ila za su kammala janyewarsu daga wasu yankuna a cikin Gaza zuwa wajen da aka ambata “layin rawaya,” kamar yadda aka amince a cikin shirin Trump tsakanin Isra'ila da Hamas,” in ji tashar talabijin ta Isra'ila Channel 12 a ranar Juma’a.

Ta kara da cewa: “Ana sa ran sojojin za su janye zuwa gabas daga Rafah da Khan Younis (kudu) da kuma daga wasu yankuna a arewacin Gaza, suna kusantar iyakar Isra'ila.”

Da safiyar Alhamis, Trump ya sanar da cewa Isra'ila da ƙungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas sun cim ma matsaya kan mataki na farko na shirin tsagaita wuta da musayar fursunoni.

Wannan yarjejeniya ta biyo bayan kwanaki hudu na tattaunawar kai-tsaye tsakanin anɓgarorin biyu a birnin Sharm el-Sheikh na Masar, tare da halartar wakilai daga Turkiyya, da Masar da Qatar, karkashin sa idon Amurka.

Rumbun Labarai
Hare-haren Isra'ila a Gaza sun kashe mutane 91, ciki har da yara 24, duk da tsagaita wuta
Netanyahu ya ba da umarnin a kai 'hare-hare masu karfi' kan Gaza
Shin Trump zai yanke alaka da Isra'ila idan ta ci gaba da mamaye Gabar Yammacin Kogin Jordan?
Amurka ta tsare ɗan jaridar Birtaniya Musulmi mai suna Sami Hamdi saboda sukar Isra'ila
Fiye da tan miliyan 61 na tarkace da baraguzai sun rufe Gaza a shekara biyu na yakin Isra'ila: UNRWA
Kalaman Trump na lalata cibiyoyin nukiliyar Iran 'mafarki ne': Khamenei
Wata ƙungiyar bayar da agaji ta Turkiyya ta ƙaddamar aikin kwashe ɓaraguzai a arewacin Gaza
Sojojin Israila sun buɗe wuta kan wasu manoma Falasɗinawa a yayin da suke girbe zaitun a Gaɓar Yamma
Mene ne abu na gaba a shirin zaman lafiya na Gaza?
Isra'ila ta sake buɗe mashigar Rafah don bai wa manyan motocin kayan agaji damar shiga Gaza
Turkiyya, Masar, Qatar da Amurka sun sa hannu kan takardar yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Dauwamammen zaman lafiya zai samu ne kawai ta hanyar kafa ƙasashe biyu, Erdogan ya faɗa wa Starmer
Sojojin Hamas sun kashe mutum 32 cikin 'gungun' da ke sace kayan agaji a Gaza
Hamas ta kammala sakin 'yan Isra'ila 20 da ta tsare a matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wuta
Wani bidiyo ya nuna yadda Isra'ila ke cin zarafin fursunonin Falasɗinawa gabanin sakin su
Trump, Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza a birnin Sharm el-Sheikh a ranar Litinin
Sojojin Amurka sun isa Isra'ila domin sa ido kan aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta ta Gaza
Gwamnatin Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza ta Trump
Shekaru biyu na kisan kiyashin Isra'ila a Gaza: Falasdinawa suna shan yunwa da cin-amana
Cikin hotuna: Falasdinu ta cika shekara ta biyu ta kisan ƙare-dangi na Israila a Gaza