| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Majalisar Wakilan Nijeriya ta amince da ƙudirin kafa 'yansandan jihohi
Wannan mataki zai taimaka wajen ƙara kusancin tsarin ‘yansanda da yanayin abubuwan da ke faruwa a yankunansu, yayin da hukumomi ke neman hanyoyin magance matsalolin tsaro daban-daban da suka mamaye tsarin da kuma iko da ake samu daga sama.
Majalisar Wakilan Nijeriya ta amince da ƙudirin kafa 'yansandan jihohi
Majalisar wakilai ta Nijeriya ta amince da kudirin kafa rundunar 'ansandan joihohi / AP

Majalisar Wakilan Nijeriya ta amince da wani kudiri a ranar Alhamis, wanda ya share fage ga jihohi 36 ciki har da babban birnin kasar su kafa rundunar 'yan sandansu, wani mataki da aka daɗe ana muhawara a kai da nufin magance matsalar rashin tsaro a Nijeriya.

Wannan mataki zai taimaka wajen ƙara kusancin tsarin ‘yansanda da yanayin abubuwan da ke faruwa a yankunansu, yayin da hukumomi ke neman hanyoyin magance matsalolin tsaro daban-daban da suka mamaye tsarin da kuma iko da ake samu daga sama.

Magoya bayan tsarin, ciki har da Shugaba Bola Tinubu, suna ganin raba iko tsakanin gwamnatin tarraya da na jihohi a bangaren ‘yansanda yana da matukar muhimmaci wajen daukar matakai ga matsalolin tsaro da suka hada da tayar da zaune tsaye da sace-sacen jama’a don ƙarban kuɗin fansa da kuma rikicin kabilance da sauransu waɗanda suka bazu a yawancin sassan Nijeriya.

Mafi yawan 'yan majalisar wakilan Nijeriya sun kada kuri'a kan ƙudirin kundin tsarin mulki yayin da ake sa ran Majalisar Dattawa za ta amince da shi kuma ta zartar daga baya a ranar Alhamis.

Wannan gagarumin mataki ne da zai bai wa gwamnatocin jihohi 36 na Nijeriya damar kafawa da kuma kula da rundunar 'yansandansu tare da sauran waɗanda ake da su na tarayya.

Dokar, wadda ta samu goyon baya daga ‘yan jam'iyyu daban-daban, kazalika dole ne ta samu amincewa daga akalla kashi biyu bisa uku na dukkan majalisun jihohi kafin ta fara aiki.

A lokuta da dama gwamnonin jihohi sun sha bayyana cewa ana dora musu alhakin tsaro amma a zahiri ba su da ikon yin kataɓus ko nuna iko da ‘yansanda a jihohinsu.

Haka kuma masu fafutukar kawo sauyi sun bayyana cewa 'yansandan jihohi za su iya taimaka wajen inganta lokutan mayar da martani, ƙarfafa tattara bayanan sirri da kuma tura jami'ai waɗanda suka fi sanin al'ummomin yankin.

Yayin da masu sukar mataki ke gargaɗin cewa, gwamnoni za su iya amfani da 'yan sandan jihohi ta hanyar da bata dace ba kan abokan hamayya ko tsiraru.

Kazalika akwai tambayoyi kan kuɗaɗen tallafi, da matakan horo da kuma haɗin gwiwa a tsakani, inda masu sharhi suka ce jihohi marasa karfi na iya fuskantar tsaiko wajen gudanar da ayyukan ‘yansandan.

Rumbun Labarai
Matatar mai ta Dangote ta fara dakon fetur kyauta zuwa wasu jihohin Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta buƙaci a soke shirin gyaran hali na tubabbun 'yan Boko Haram
Jihar Legas ta kama mabarata 396, tana tantance bayanansu domin mayar da su jihohinsu na asali
Nijeriya za ta binciki manyan kamfanonin fasaha kan amfani da labaran ƙasar ba bisa ƙa’ida ba
Gwamnatin Nijeriya ta bai wa 'yan ƙasarta damar ƙarshe ta kwashe su daga Afirka ta Kudu
‘Yansandan Nijeriya sun dakile harin ‘yanbindiga a Sokoto
Yadda matsalar tsaron Nijeriya ke ƙara barazana ga wadatar abinci
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da fara ayyukan Bama zuwa Banki da Dikwa zuwa Gamboru-Ngala
Hukumar INEC ta Nijeriya ta tsawaita aikin rajistar masu zaɓe da makwanni biyu
Kotu ta samu mutum biyu da laifin ta'addanci a Nijeriya
Nijeriya ta ƙaddamar da masana'antar sarrafa lithium mafi girma a Yammacin Afirka a jihar Nassarawa
Amurka ta janye akasarin sojojinta da ta aika Nijeriya
Yunwa ta kai mummunan mataki da bai taɓa kai wa ba a shekaru 10 a Arewacin Nijeriya - WFP
Sojojin Nijeriya sun kashe ’yanta’adda 662, sun ceto 951 da aka sace cikin watanni uku
CBN ya soke lasisin ƙananan bankuna na Microfinance 46 saboda rashin cika ƙa’idoji
Nijeriya ta yi alƙawarin tallafa wa 'yan ƙasar 271 da suka dawo daga Afirka ta Kudu
Ɗan Nijeriya ya mutu bayan sakinsa daga kurkuku a Côte d'Ivoire
Gwamnatin Nijeriya ta karɓi 'yan ƙasar 269 da aka sake mayarwa gida daga Afirka ta Kudu
Jam'iyyar adawa ta NDC a Nijeriya ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin kotu game da rajistarta
Sojojin Nijeriya sun ceto ɗalibai da malaman GDSS Lassa 10 a Jihar Borno