| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Aikin matatar man Dangote zai ci gaba a gaɓar tekun Kenya, a cewar Shugaba Ruto
Shugaba William Ruto ya ce aikin wanda attajirin Nijeriya Aliko Dangote ke mara wa baya zai samar da ayyukan yi 60,000 tare da samar da mai a ƙasashen Afirka 8.
Aikin matatar man Dangote zai ci gaba a gaɓar tekun  Kenya, a cewar Shugaba Ruto
TSOHON HOTO: Shugaban rukunin kamfanonin Dangote , Aliko Dangote

Shugaban Kenya William Ruto ya bayyana ranar Jumma’a cewa shirye-shirye na abin da ake tsammanin za ta kasance matatar mai mafi girma a gabashin Afirka na dab da ci gaba bayan tattaunawa da attaijirin Afirka ɗan Nijeriya, yana mai cewa aikin zai samar da ayyuka kimanin 60,000 ga matasa ‘yan Kenya.

Da yake magana wajen ƙaddamar da mataki na biyu na shirin tallafin gwamnati na Nyota, Ruto ya ce shi ya cim ma wata yarjejeniya da Dangote ta ci gaba da aikin matatar mai, wadda za a gina a jihar Lamu da ke gaɓar teku, kimanin nisan kilomita 470 ( mil 292 ) kudu maso gabas da babban birnin ƙasar Nairobi.

“A yanzu Kenya za ta gina matatar gabashin Afirka a nan Lamu, inda za mu buƙaci matasa 60,000 su yi aiki,” a cewar Ruto.

“Na yi magana da mai zuba jari Aliko Dangote, kuma mun cim ma matsaya cewa matatar man ba kawai Kenya za ta yi wa hidima ba, za ta yi aiki wa Ethiopia da Sudan Ta Kudu da Uganda da Tanzania da Rwanda da Burundi da kuma Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kongo, yayin da za ta samar da damarmaki na ayyukan yi ga matasa,” a cewarsa.

Cibiyar makamashi ta yanki

Ruto ya ce matatar za ta mayar da Kenya wata cibiyar makamashi ta yanki ta hanyar samar da kayayyaki na man fetur da sinadirai a faɗin gabashi da tsakiyar Afirka yayin da za ta rage dogaron yankin kan tataccen mai da ake shiga da shi.

Aikin ya biyo bayan shawarar da masana’antar Dangote ta yanke ne wajen kafa matatar man a Lamu, lamarin da ya kawo ƙarshen watanni da aka shafe ana jita-jita kan ko za a gina ta a Kenya ko Tanzania.

Matatar, mai girman tace gangar mai 700,000 a kowace rana ana tsammanin za ta kasance matata mafi girma ne a gabashin Afirka da kuma tallafa wa ci-gaban masana’antu a kewayen hanyar Lamu da Port-South da Sudan zuwa Ethiopia (LAPSSET), wani muhimmin abin more rayuwa na yanki da ke haɗa gaɓar tekun Kenya zuwa ta ƙasashe maƙwabta.

Kamfanin ya ce ana tsammanin aikin gina matatar zai ɗauki kimanin watanni 30 da zarar an fara yinsa.

An zaɓi Lamu ne saboda muhimmancin wurin da yake a bakin tekun Indiya da tashar jiragen ruwa mai zurfi da kuma kusanci da hanyoyin tafiya da wasu ƙasashen gabashi da tsakiyar Afirka mara gaɓar teku ke amfani da su.

Rumbun Labarai
Ƙoƙarin kawar da sankarau: Manufar Afirka ta kawar da cutar baki ɗaya nan da 2030
Mutane fiye da 4,000 ne suka kamu da cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo - Gwamnati
Kwamitin tattaunawa na Libiya ya cim ma matsaya kan tsarin ɗaukar shugaban hukumar zaɓe
Gargadin shugabannin Afirka kan cin abinci a makare da illolin shan siga da giya
Shugaba Biya na Kamaru ya yi sauye-sauye a shugabancin sojin ƙasar
Ghana ta amince da ɗaurin shekara 20 ga duk wanda ya mayar da gonar koko zuwa wani abu daban
Ɗaruruwan mutane sun yi hijira daga kudu maso yammacin Nijar saboda hare-haren 'yanta'adda
‘Yan Boko Haram sun kashe sojojin Nijar, in ji kafar watsa labaran gwamnati
Fitacciyar mawaƙiyar Afirka Ta Kudu ta soke kalankuwarta a Legas bayan an kori baƙi daga ƙasarta
Gwamnatin Ghana ta amince da shawara ƙara wa'adin mulkin shugaban ƙasa
Adadin 'yan ci-ranin da suka rasu ya kai 19 bayan dubbai sun tsallaka zuwa yankin Ceuta na Sifaniya
Biranen Afirka 25 da Amurka za ta rufe ayyukan bayar da biza daga ranar 1 ga Agustan 2026
Siyasar Kamaru: Ina Shugaba Paul Biya ya shiga?
Nijar ta dakatar da kamfanonin dillancin siminti 36 kan zargin ɓoye shi don haddasa ƙarancinsa
Hukumomin Libya a Benghazi sun kori baƙin-haure fiye da 117,000 daga ƙasar
Mutumin da ya fi kowa tsawo a Ghana Awuche ya rasu
Chadi ta sanar da shirin fita daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC)
An gudanar da zanga-zanga a Tripoli saboda tsadar rayuwa da tabarbarewar ayyukan gwamnati
Ƙarin ma'aikatan jinya sun shiga yajin aiki yayin da cutar Ebola ta kama kusan mutum 3,000
Yara na cikin waɗanda aka kashe a harin jirgi marar matuƙi a wata kasuwar Sudan