| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
EFCC ta janye ƙarar da ta shigar da Maryam Shehu da Abubakar Shuraim kan zargin ɓata suna
Sakin nasu ya zo ne a daidai lokacin da lauyoyin Maryam suka shigar da buƙatar bayar da belinta don samun damar rubuta jarrabawar shekarar karshe a jami’a, kamar yadda ɗaya daga cikin lauyoyin Abba Hikima ya bayyana a shafinsa na Facebook.
EFCC ta janye ƙarar da ta shigar da Maryam Shehu da Abubakar Shuraim kan zargin ɓata suna
Maryam ɗaliba ce ta shekarar ƙarshe a jami'ar Bayero ta Kano / FB: Abba Hikima

Shugaban Hukumar Yaƙi da Yi wa Tattalin Arzikin Nijeriya Zagon Ƙasa (EFCC), Olanipekun Olukoyede ya ba da umarnin janye ƙarar da hukumar ta shigar da wasu matasa biyu, Maryam Shehu da Abubakar Shuraim Abdulhamad, kan ɓata wa EFCC suna, kamar yadda sanarwar hukumar ta bayyana.

Shugaban na EFCC ya ce ya yi hakan ne don tausayawa matasan, waɗanda aka gurfanar a gaban Babbar Kotun Tarayya a Abuja, ranar 20 ga Agustan 2026.

An zarge su ne da aikata laifuka a intanet, da yaɗa bayanan ɓata-suna ga hukumar ta EFCC, lamarin da ya janyo suka daga wasu ‘yan Nijeriya, da kuma neman afuwa daga mahaifin Maryam Shehu.

Sakin nasu ya zo ne a daidai lokacin da lauyoyin Maryam suka shigar da buƙatar bayar da belinta don samun damar rubuta jarrabawar shekarar karshe a jami’a, kamar yadda ɗaya daga cikin lauyoyin Abba Hikima ya bayyana a shafinsa na Facebook.

Maryam dai tana shekarar ƙarshe ne a Jami’ar Bayero da ke Kano.

A ranar Talata ne lauyan ya wallafa wata buɗaɗɗiyar wasiƙa ga ministan shari’a na Nijeriya yana kira a gare shi ya sa baki don ganin EFCC ta saki Maryam ko kuma ta gurfanar da ita a kotu.

Abba Hikima ya yi zargin cewa EFCC ta tsare Maryam fiye da kwanaki 30 ba tare da gabatar da ita a kotu ba, abin da ya ce ya saɓa wa dokokin ƙasar.

A ranar Laraba ne kuma EFCC ta gurfanar da Maryam da Shuraim a kotu kan zargin ɓata suna.

Batun dai ya janyo ce-ce-ku-ce a kafofin sada zumunta, inda lauyoyi da masu fafutuka irin su Omowele Sowere suka shiga fafutuka da kiraye-kirayen a sake su.  

Sowere, wanda ya halarci zaman kotun a ranar Alhamis lokacin da aka gurfanar da su Maryam, ya ce suna fatan kotun za ta zauna a yau Juma’a ko da ɗan taƙaitaccen zama ne, don a samu damar sakin Maryam, ta yadda za ta samu damar rubuta jarrabawar da za a fara ranar Asabar.