| Hausa
WASANNI
2 minti karatu
Toni Kroos ya soki gasar ƙwallo ta Saudiyya game da raina tasirin Ronaldo
Tuni aka fara raɗe-raɗin ƙungiyoyin da Ronaldo zai iya komawa, saboda rashin jin daɗinsa da irin goyon bayan da hukumomin Saudiyya ke bai wa ƙungiyarsa.
Toni Kroos ya soki gasar ƙwallo ta Saudiyya game da raina tasirin Ronaldo
Tun a 2023 ne Cristiano Ronaldo ya koma taka leda a Saudiyya. / Reuters
9 Fabrairu 2026

Tsohon ɗanwasan Real Madrid wanda ya yi wasa da Cristiano Ronaldo tsawon shekaru, ya nemi a girmamam matsayin gwarzon ɗanwasan saboda gudunmawar da ya bai wa tamola.

Da yake magana kan taƙaddamar da ke tsakanin Ronaldo da hukumar da ke kula da babbar gasar ƙwallo ta Saudiyya, Kroos ya soki gasar yana mai nuna muhimmancin Ronaldo.

Kroos, wanda ɗan asalin Jamus ne, yana cewa zuwan Ronaldo ƙungiyar Al-Nassr ta Saudiyya shi ne abin da ya kawo babban sauyi a tagomashin gasar a fagen ƙwallo na duniya.

“Gasar Saudi Pro League ta zama wata iri. Ba wanda ya san da ita kafin Cristiano Ronaldo ya je can, amma yanzu suna raina tasirin mutumin da ya fito da su duniya. Ba domin Ronaldo ba, gasar Saudiyya da ta rasa farinjinta”, in ji Kroos.

Dalilin da ya sa Kroos ke kare tsohon abokin wasan nasa shi ne cewa, kada a raina tallafin da Ronaldo ya bai wa gasar ta Saudiyya.

Taƙaddama da Ronaldo

A farkon watan nan ne rahotanni suka nuna cewa an fara yin tababa kan ci gaba da kasancewar Cristiano Ronaldo a ƙungiyar Al-Nassr, da ma gasar ta Saudiyya ɗungurungun.

Duk da cewa Cristiano Ronaldo yana da kwantiragi da za ta kai har 2027, rahotanni na nuna cewa zai iya barin Saudiyya a bazara mai zuwa saboda Karim Benzema ya koma Al-Hilal daga Al-Ittihad.

Tuni aka fara raɗe-raɗin ƙungiyoyin da Ronaldo zai iya komawa, saboda rashin jin daɗinsa da irin goyon bayan da hukumomin Saudiyya ke bai wa ƙungiyarsa.

Sakamakon taƙaddamar Ronaldo ya ƙauracewa wasanni biyu da ƙungiyarsa ta buga a baya-bayan nan, tare da Al-Riyadh da kuma Al-Ittihad.

Rumbun Labarai
Ina Mo Salah zai koma daga Liverpool?
Nijeriya ta doke Iran a wasan sada zumunta da suka buga a Turkiyya
Lukaku ya ƙi komawa atisaye a Napoli bayan janyewa daga buga wa ƙasarsa Belgium wasa
Batun kofin AFCON: Me zai faru da ƙwallon ƙafa a Afirka bayan tataɓurza kan Senegal?
'Yanwasan Super Eagles 21 sun isa birnin Antalya na Turkiyya don wasannin sada zumunta
Mbeumo da Sesko na Man United ba za su je buga wa kasashensu wasan sada zumunta ba
Senegal za ta daukaka ƙara kan hukuncin ƙwace mata Kofin AFCON 2025
Tsohon golan Manchester United, Sergio Romero, ya yi ritaya daga kwallo
Joan Laporta ya sake zama shugaban Barcelona bayan lashe zaɓe
Trump ya sa tawagogin kasashen Afirka cikin matsala a gasar Kofin Duniya na FIFA 2026
Barcelona za ta ƙwato Haaland daga Manchester City don maye gurbin Lewandowski
Courtois ya jajanta wa golan Tottenham da aka ci ƙwallo 3 a minti 16 da fara wasa
Ƙwallon da Galatasaray ta zura a raga a farkon wasa ya nutsar da Liverpool a karawar Zakarun Turai
An haramta wa ɗanwasan Ghana buga ƙwallo har abada saboda caca a Gasar MLS ta Amurka
Lewandowski ya ce 'daina cin kayan zaƙi' ne ya sa shi yin ƙarko zuwa yanzu
An dakatar da Gasar Kofin Afirka ta Mata a Maroko bayan wasu tawagogi sun fara isa ƙasar
CAF ta tabbatar da ranakun buga wasannin kwatafainal na Kofin Zakarun Afrika
Real Madrid na shirin ɗauko Allegri don maye gurbin Arbeloa
Ronaldo ya dauke jirginsa daga Saudiyya zuwa Madrid bayan harin Iran a Riyadh
Nijeriya za ta buga wasan sada zumunta da Iran a Maris ɗin nan