Hukumar Kula da 'Yan Gudun Hijira ta Duniya (IOM) a ranar Lahadi ta yi gargadin cewa babban birnin Jihar Kordafan ta Arewa wato Al Obeid na Sudan, zai iya faɗawa cikin irin mummunan yanayin da yankin Al Fasher da ke maƙwabtaka da shi ke ciki idan dakarun RSF suka ci gaba da kai hare-hare.
Gargaɗin ya fito ne a cikin wani saƙon bidiyo da IOM ta wallafa a shafinta na X, wanda Mohamed Refaat, babban jami'in ofishin hukumar a Sudan ya karanto.
"Duk muna cikin damuwa kan cewa Al Obeid zai iya zama Al Fasher na gaba... Idan ba mu ɗauki mataki yanzu ba, za mu sake ganin wani Al Fasher," in ji Refaat.
Ya kara da cewa sama da mutane 500,000 a Al Obeid suna bukatar taimakon jinƙai.
Munanan Laifuka
Refaat ya kuma ce Tawagar Samar da Mafaka a Sudan, wacce IOM ke jagoranta, na "ɗaya daga cikin ƙungiyoyin da ba su da isassun kudade a Sudan," yanayin da ke takaita ikonta na samar da taimako ga iyalan da abin ya shafa.
Kusan wata guda kenan da Al Obeid ke fuskantar hare-haren jiragen sama marasa matuka na RSF wadanda ake kai wa kan babban tashar wutar lantarki ta birnin, wuraren mai da sauran wuraren fararen hula, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama.
A ranar Juma'a, Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargaɗi kan wani sabon bala'i na kare hakkin dan adam da ke faruwa a Al Obeid kuma ta yi kira ga RSF da ta dakatar da hare-haren da take kai wa birnin.
Kazalika gargaɗin ya biyo bayan ƙaruwar damuwa daga MDD, da ƙungiyoyin yankin da Amurka kan rahotannin tarin sojojin RSF a kusa da Al Obeid da kuma hadarin aikata munanan laifuka.
Keta haddi
A cewar ƙungiyoyin cikin gida da na ƙasa da ƙasa, kama Al Fasher da RSF ta yi a ranar 26 ga Oktoba, 2025, ya biyo bayan rahotannin cin zarafi da aka yi wa fararen-hula da kuma gargaɗin cewa yanayin zai iya kawo cikas ga rarrabuwar kawuna a Sudan.
A ranar 29 ga Oktoba, 2025, kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo, wanda aka fi sani da Hemedti, ya amince cewa an aikata "keta haddi" a Al Fasher kuma ya sanar da kafa kwamitocin bincike.
MDD ta kuma yi gargaɗi a ranar 12 ga watan Mayu game da ƙaruwar hare-haren jiragen sama marasa matuƙa a yankin Kordofan, tana mai cewa hare-haren sun kashe aƙalla fararen-hula 880 tsakanin watan Janairu zuwa Afrilun 2026.















