Sama da mutane 4,500 ne suka rasa matsugunansu a jihohin Arewacin Darfur da Blue Nile na Sudan, a cikin mawuyacin hali na rashin tsaro, in ji Hukumar Kula da 'Yan Gudun Hijira ta Duniya (IOM).
A Arewacin Darfur, hukumar ta Majalisar Dinkin Duniya ta faɗa a ranar Laraba cewa ƙungiyoyin sa ido kan matsugunan sun ƙiyasta cewa kimanin mutane 1,275 sun tsere daga kauyukan Gorbora da Wadi Arkawi a yankin Um Baru tsakanin 3 zuwa 6 ga Satumba.
Iyalan da suka rasa matsugunan sun koma yankin Karnoy da ke Arewacin Darfur, yayin da wasu suka tsallaka kan iyaka zuwa maƙwabciyar ƙasar, Chadi.
IOM ta ce lamarin yana ci gaba da "yin tsanani da rashin tabbas," kuma tana ci gaba da sa ido sosai kan abubuwan da ke faruwa.
A wani ɓangaren kuma, hukumar ta ce kimanin mutane 3,315, daidai da iyalai 663, sun rasa matsugunansu a cikin kwana ɗaya daga ƙauyuka da dama a yankin Geisan da ke kudu maso gabashin jihar Blue Nile ta Sudan saboda taɓarɓarewar tsaro.
An sami rahoton korar 'yan gudun hijira a ranar 7 ga Satumba daga ƙauyuka da dama, ciki har da Abu Shneina, Rabaa da Wadi Arab. Iyalan da abin ya shafa sun koma yankin Wad al-Mahi da ke cikin jihar Blue Nile.
Hukumar IOM ta ce sabon gudun hijirar ya biyo bayan wani hari da aka kai a baya a ranar 5 ga Satumba.
A ranar Lahadi, hukumar ta ce an sake samun wasu mutane 1,690 da suka rasa matsugunansu daga ƙauyuka uku a yankin Kurmuk na Blue Nile saboda ƙaruwar tashin hankali.
Blue Nile ta shaida karuwar sojoji a cikin 'yan kwanakin nan sakamakon hare-haren da dakarun sa-kai na (RSF) da ƙawayenta, ƙungiyar 'yantar da al'ummar Sudan (SPLM-N), suka kai a yankuna da dama.
A ranar 4 ga Satumba, hukumomi a Kurmuk sun ce sojojin Sudan sun daƙile wani hari da RSF da SPLM-N suka kai a yankin Al-Baraka.
Tun daga ƙarshen watan Yuni, ƙauyuka a yankin Um Baru na Arewacin Darfur suma sun fuskanci hare-haren da aka ɗaura alhakinsu a kan, ciki har da kai hari a kasuwanni da ƙonawa da sace-sace a ƙauyuka, a cewar ƙungiyoyin kare haƙƙin bil'adama da ƙungiyoyi na Sudan.
Sudan ta faɗa cikin yaƙin da ake yi tsakanin sojoji da RSF tun daga watan Afrilun 2023, inda aka kashe dubban mutane tare da korar kimanin mutane miliyan 13, a cewar ƙiyasin Majalisar Dinkin Duniya da na ƙasa da ƙasa.

















