RSF ta kashe ƙananan yara a harin da ta kai wani masallaci a yankin Kordofan na Sudan

Kai hare-haren kan ƙananan yara a cikin masallatai "alama ce da ke nuna ƙaruwar cin zarafin fararen hula," kamar yadda ƙungiyar likitocin Sudan ta bayyana.

By
Hukumar lafiya ta duniya (WHO) ta ce yaƙin ya kashe aƙalla mutum 40,000 tare da raba mutum miliyan 12 da gidajensu. / AP

Wani harin jirgi mara matuƙi a kan wani masallaci ya kashe yara biyu tare da jikkata wasu 13 a yankin Kordofan da ke tsakiyar Sudan da safiyar ranar Laraba, a cewar wata ƙungiyar likitoci, yayin da yaƙin basasar ƙasar yake ci gaba da ƙamari.

Ƙungiyar Sudan Doctors Network, wadda ke sa ido kan rikicin, ta ce dakarun RSF da ke yaƙar sojin ƙasar, ne suka kai harin a birnin al Rahad a Jihar North Kordofan.

Mai magana da yawun ƙungiyar Mohamed Elsheikh ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Associated Press cewa yaran suna halartar karatun Alƙur’ani da safiya ne lokacin da lamarin ya faru.

Kai hare-haren kan yara cikin masallatai "wata alama ce da ke nuna ƙaruwar cin zarafin fararen-hula,” in ji ƙungiyar.

“Har yanzu babu zaman lafiya a Kordofan ”

Yaƙi tsakanin rundunar RSF da sojin ƙasar ya ɓarke ne a shekarar 2023, bayan da dakarun RSF suka ƙi amincewa a shigar da su rundunar sojin ƙasar.

Hukumar lafiya ta duniya (WHO) ta ce yaƙin ya kashe aƙalla mutum 40,000 tare da raba mutum miliyan 12 da gidajensu.

Ƙungiyoyin ba da agaji sun ce gaskiyar adadin waɗanda suka mutu a rikicin zai iya ruɓanya hakan sau da yawa, yayin yaƙin a wurare da yawa da wurare masu nisa ke tare hanya.

Ƙungiyar Sudan Doctors Network ta bayyana hare-hare kan wuraren ibada a matsayin wani ɓangare na “tsararren yanayi” da ke zagon ƙasa ga tsarkin wuraren addini.

An lalata, ƙona ko kuma kai harin bam kan fiye da masallatai 15 yayin da aka ƙona ko kai harin bam kan wani ɓangare na fiye da coci-coci 165 a yaƙin, a cewar alƙaluman da aka fitar a shekarar da ta gabata .

Hare-haren jirage maras matuƙa sun zama ruwa dare a ƙasar.

Ranar Lahadi, wani harin jirgi maras matuƙi na RSF ya samu wata mota ɗauke da wasu iyalan da aka raba da muhallansu a tsakiyar Sudan, inda ya kashe aƙalla mutum 24 , ciki har da yara takwas, in ji ƙungiyar Sudan Doctors Network.

Kwamishinan kare ‘yancin ɗan’adam na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ya ce kawo yanzu yankin Kordofan "mai tashin hankali da kuma inda hamayya ta mayar da hankali” yayin da ɓangarorin da ke yaƙi suke neman karɓe iko da muhimman wurare.