Cibiyar Al’adu ta Yunus Emre ta haɗa Turkiyya da Nijeriya ta hanyar fasaha

Masu ayyukan fasaha daga Turkiyya da Nijeriya sun haɗu a Cibiyar Al’adu ta Yunus Emre da ke Abuja domin baje-kolin al’adu masu dangantaka da bambance-bambance na fasaha a ƙarƙashin manufa ɗaya.

By
Hotuna da aka nuna a baje kolin Cibiyar Yunus Emre da ke Abuja. / TRT Afrika English

An ƙaddamar da baje-kolin “İki Áşá – Al’adu biyu, manufa ɗaya” a Cibiyar Al’adu ta Yunus Emre da ke Abuja, wadda ta haɗa kan kan masu fasaha daban-daban daga Turkiyya da Nijeriya domin baje-kolin al’adu masu dangantaka da bambance-bambance na fasaha a ƙarƙashin manufa ɗaya.

An shirya baje-kolin ne a Cibiyar Al'adu ta Yunus Emre da ke Abuja, wadda Fatih Erkin Mahdum ke jagoranta, tare da haɗin gwiwar Ofishin Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Fasaha, Al'adu da Tattalin Arzikin Kirkire-Ƙirkire na Nijeriya, da kuma a haɗin gwiwa da Ayomide Adeagbo.

Baje-kolin ya samu baje ayyuka da suka haɗa da na Farfesa Dakta Tuna Akcay daga Turkiyya da masu ɗaukar hoto na Nijeriya waɗanda suka haɗa da Sope Adelaja da Anigbogu Ozioma Uche.

Ta hanyar kyamarorinsu, masu fasahar sun gabatar da hotuna masu ɗaukar hankali – waɗanda suka haɗa da muhimman wurare na yankunan Turkiyya zuwa ga bikin al’adu na Nijeriya da kuma kyawawan abubuwa na ƙasar – inda suke nuna irin abubuwan al’adu da za a iya tunawa da su na duka ƙasashen.

Jakadan Turkiyya a Abuja, Mehmet Poroy, ne ya bude-baje kolin hukuma ta hanyar yanke ribbon, tare da wakilai daga cibiyoyin diflomasiyya da al'adu.

Taron ya kuma ba wa masu halarta dama don su yi nazari kan muhimmancin wannan haɗin gwiwa.

Mai ɗaukar hoto Sope Adelaja ya bayyana baje-kolin a matsayin wata dama mai ma'ana sosai. Ya ce cibiyar al'adu ta Turkiyya tana samar da muhimmin dandali ga masu fasaha daga wurare daban-daban su taru, su kalli ayyuka daga al'adu na Turkiyya da na Nijeriya, kuma su fahimci labaran da ke tattare da ayyukan.

“Fasaha tana gina gada inda kalmomi wasu lokuta ba za su iya ba, tana ƙarfafa alaƙar al'adu kuma tana zurfafa dangantaka tsakanin Turkiyya da Nijeriya,” in ji Adelaja a tattaunawarsa da TRT Afrika.

Ya ƙara da cewa ganin ayyukansa an nuna su a Cibiyar Yunus Emre yana da matuƙar ma'ana a gare shi, saboda a ko yaushe yana da ƙwarin gwiwa wajen haifar da tasiri mai ma'ana ta hanyar fasaharsa.

Ya lura cewa baje kolin ba kawai nuna ayyuka ba ne, har ma game da “raba labarai, da abubuwa na motsin zuciya da ƙwarewar rayuwa ga masu kallo da suka fi yawa,” yana kirkirar wata dama inda al'adun biyun za su iya fahimtar juna da su yaba wa juna.

Sunan “İki Áşá” yana nuna haɗuwa ne ta abubuwan harshe na Yarabawa da na Turkiyya, yana alamta haɗuwar al'adu biyu a ƙarƙashin manufa ɗaya.

Tun daga buɗe ofishinsa na farko a ƙasashen waje a shekarar 2009, Cibiyar Yunus Emre ta faɗaɗa zuwa cibiyoyi 92 a ƙasashe 68, tana tallata harshen Turkiyya, fasaha da al'adunta a duniya.

Ta hanyar kwasa-kwasan da ake yi na koyon harshe, baje-kolin da shirye-shiryen ilimi na inganta tattaunawa da musayar al'adu da ƙarfafa dangantaka mai ɗorewa tsakanin Turkiyya da al'ummomi a faɗin Afirka da ma sauran ƙasashe.