Amurka ba ta da masaniya kan harin da Isra’ila ta kai filin iskar gas na South Pars a Iran - Trump

Shugaban Amurka ya bayyana cewa Isra’ila ba za ta sake kai hari kan South Pars ba sai dai idan Iran ta mayar da martani, yayin da yake barazanar lalata dukkan wurin idan Iran ta sake kai wa Qatar hari.

By
Trump ya yi gargaɗin kan ƙarin hare-hare kan kayayyakin iskar gas ɗin Qatar , yana mai nuna ƙaddamar da ramuwar gayyar Amurka / Reuters / Reuters

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi ikirarin cewa Amurka ba ta da masaniya game da harin da Isra’ila ta kai wa filin iskar gas na South Pars da ke Iran.

Ya bayyana cewa Isra’ila ba za ta sake kai wani harin ba sai dai idan Tehran ta mayar da martani, yana mai barazanar cewa duk wani hari na gaba kan ayyukan iskar gas (LNG) na Qatar zai sa Amurka ta ruguza daukacin wurin.

“Amurka ba ta san komai game da wannan harin (kan filin iskar gas na South Pars) ba, kuma kasar Qatar ba ta da hannu a cikinsa ta kowace fuska, sannan ba ta da masaniyar cewa hakan zai faru,” in ji Trump a shafinsa na Truth Social.

Wannan ikirarin nasa ya saba wa rahotannin farko da ke cewa Washington ta san da harin tun kafin a kai shi, ko da yake ba ta hannu a cikinsa.


Ya ce Iran ba ta “wani uzuri ko dalili” na kai hari kan wani sashe na matatar iskar gas ta Qatar da ke Ras Laffan Industrial City, sakamakon gazawarta wajen fahimtar gaskiyar lamarin.
Trump ya bayyana harin Isra’ila a matsayin “fusata ce ta sanya Isra’ila ta kai mummunan hari” kan wurin, yana mai cewa “wani karamin bangare ne kawai” na filin harin ya shafa.

Ya yi gargadin cewa idan aka sake taba ayyukan iskar gas na Qatar, Amurka za ta “yi babban luguden wuta a daukacin filin iskar gas na South Pars” tare ko ba tare da sa hannun Isra’ila ba, harin da Iran “ba ta taba ganin irisa ba.”

Ya kara da cewa ba ya son bayar da umarnin irin wannan barna saboda illar da za ta yi wa makomar Iran na dogon lokaci, amma ba zai yi kasa a gwiwa ba idan an tilasta masa yin hakan.

Wani harin sama da Isra’ila ta kai a wani bangaren filin iskar gas na South Pars a ranar Laraba, wanda ya dakatar da samar da iskar gas a manyan matatun mai guda biyu.

Qatar ta bayar da rahoton hare-haren makamai masu linzami guda biyu daban-daban a Ras Laffan Industrial City, babbar matatar iskar gas ta Qatar, a ranar Laraba da kuma sanyin safiyar Alhamis.

A matsayin martani, Qatar ta kori jami’an diflomasiyya na soja da na tsaro na Iran da ke ofishin jakadancinta tare da ma’aikatansu.