NIJERIYA
2 minti karatu
ASUU: Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta Nijeriya ta shiga yajin aikin gargaɗi
Shugaban ƙungiyar Farfesa Chris Piwuna ne ya sanar da hakan a lokacin wani taron manema labarai da aka gudanar a Jami’ar Abuja, a ranar Lahadi.
ASUU: Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta Nijeriya ta shiga yajin aikin gargaɗi
An shafe shekaru da dama ana samun matsala tsakanin gwamnatin tarayya da malaman na jami'o'i
12 Oktoba 2025

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya ASUU a ranar Lahadi ta sanar da shiga yajin aiki na makonni biyu, wanda zai kasance cikakke kuma gaba ɗaya, a duka jami’o’in gwamnati na ƙasar.

Shugaban ƙungiyar Farfesa Chris Piwuna ne ya sanar da hakan a lokacin wani taron manema labarai da aka gudanar a Jami’ar Abuja, a ranar Lahadi.

 “’Yan jarida abokan aikinmu, babu wani abu mai ƙarfi a yanzu da zai hana aiwatar da matsayar kwamitin zartarwa na ASUU ta shiga yajin aikin gargaɗi na makonni biyu bayan ƙarewar wa’adin kwanaki 14 da aka bayar tun ranar 28 ga Satumban, 2025.

“Saboda haka, duka rassan ASUU an umurce su da su dakatar da ayyukansu daga misalin ƙarfe 12 na daren Litinin, 13 ga Oktoban, 2025.

“Yajin aikin gargadin zai kasance cikakke kuma gaba ɗaya, kamar yadda aka amince a taron NEC na ƙarshe,” kamar yadda Piwuna ya bayyana.

Sabuwar taƙaddama tsakanin malaman jami’a da gwamnatin tarayya na zuwa ne duk da ƙoƙarin tattaunawa don kauce wa wani sabon yajin aiki a jami’o’in ƙasar.

A ranar Laraba, Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ya bayyana a Abuja cewa gwamnati ta shiga matakin ƙarshe na tattaunawa da ASUU da sauran ƙungiyoyi domin warware matsalolin da suka shafi albashi, kuɗaɗen tallafi, da aiwatar da yarjejeniyar ASUU ta shekarar 2009.

Rumbun Labarai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso
Muna shirin ɗaukar mataki kan Nijeriya - Sakataren Ma’aikatar Yaƙi na Amurka
Trump ya umarci Ma'aikatar Yaƙi ta Amurka ta soma shirin yiwuwar kai hari Nijeriya
Tinubu ya mayar da martani bayan Amurka ta ce ana yi wa Kiristoci kisan gilla a Nijeriya
Gwamnatin Nijeriya ta sake jaddada aniyarta ta yaƙi da tsattsauran ra'ayi
Samaila Bagudo: 'Yan bindiga sun sace Mataimakin Kakakin Majalisar Jihar Kebbi
Donald Trump ya ayyana Nijeriya a matsayin ƙasar da ake yi wa Kiristoci kisan gilla
‘Yan sandan Nijeriya sun ceto ‘yan kasashen waje 23 da aka yi garkuwa da su