| Hausa
KASUWANCI
3 minti karatu
Nijeriya za ta bude manyan masana'antun sarrafa ma'adanin lithium
Masana'antun, waɗanda akasarin masu zuba jari daga China ne za su kafa, za su iya taimakawa wajen haɓaka ɗimbin arzikin ma'adinan Nijeriya zuwa ga samar da ayyukan yi a faɗin ƙasar.
Nijeriya za ta bude manyan masana'antun sarrafa ma'adanin lithium
Lithium na daya daga cikin albarkatun ma'adinai da dama a Nijeriya. / AFP

Nijeriya na shirin ƙaddamar da wasu manyan masana'antun sarrafa ma’adanin lithium guda biyu a wannan shekara, kamar yadda ministan ma'adinai na kasar ya bayyana a ranar Lahadi, hakan na nuna wani sauyi da za a samu daga fitar da ainihin ma'adinai zuwa ga ƙara masa daraja a cikin gida.

 Masana'antun, waɗanda akasarin masu zuba jari daga China ne za su kafa, za su taimaka wajen mayar da ɗimbin arzikin ma'adinai da Najeriya ke da shi zuwa ga samar da ayyukan yi, da fasaha, da kuma bunƙasar masana'antu na cikin ƙasar.

Ministan ma’adinai na Nijeriya, Dele Alake ya ce, ana sa ran kamfanin sarrafa lithium da ya kai na dala miliyan 600 wanda ke kusa da kan iyakar johohin Kaduna da Neja zai fara aiki a wannan watan, yayin da ake dab da kammala aikin masana’antar sarrafa lithium wadda ta kai dala miliyan 200 da ke wajen Abuja.

Ministan ya ce ana sa ran ƙarin wasu masana'antun guda biyu a jihar Nasarawa wadda ke da iyaka da babban birnin tarayya Abuja, kafin karshen shekarar 2025.

"Yanzu muna mayar da hankali ne wajen mayar da arzikin ma'adinanmu zuwa ga darajar tattalin arzikinmu na cikin gida da samar ayyuka yi da fasaha, da kuma masana'antu," in ji Alake.

Faɗaɗa gyare-gyaren haƙar ma'adinai a Nijeriya

Bisa ga wasu sanarwa daban-daban da gwamnonin jihohin da masana’atun suke, sama da kashi 80 cikin 100 na kuɗaɗen da aka kafa su sun fito ne daga ƙasar China, ciki har da kamfanin hakar ma'adinai na Jiuling Lithium da Canmax Technologies.

Sauran hannayen jarin kuma mallakin kamfanin Three Crown Mines ne na cikin gida.

Yunƙurin samar da masana’atar sarrafa ma’adanin na cikin gida ya biyo bayan wani bincike da hukumar kula da yanayin ƙasa ta Nijeriya ta gudanar a shekarar 2022, wanda ya gano tarin ma’adinin lithium mai daraja a kusan rabin jihohin da ke kasar, wanda ya jawo hankulan ƙasashen duniya.

Waɗannan ci-gaban wani bangare ne na faɗaɗa sauye-sauyen da Nijeriya ke yi a ɓangaren hako ma'adinai da aka bari a baya, wanda a halin yanzu ke ba da gudummawar ƙasa da kashi ɗaya cikin ɗari na yawan kuɗaɗne da ƙasar ke samu.    

Sauran gyare-gyaren da aka sa a gaba sun haɗa da takaita fitar da ma’adanai da ba a sarrafa su ba zuwa kasashen waje, da kuma tsara ayyukan haƙo ma’adanan, wadanda ke samar da mafi yawan ayyukan hannu da ake yi a halin yanzu, tare da kafa kamfanonin haƙar ma’adinai na jiha inda masu zuba jari za su mallaki hannun jari har kashi 75%.

Rumbun Labarai
Shigar kuɗaɗe daga waje cikin Nijeriya don zuba jari ta ƙaru da kusan kashi 90% a 2025 – Hukumomi
Hauhawar farashin mai ta janyo aiki daga gida da karatu daga nesa a wasu ƙasashen Asiya
Harin da aka kai wa 'yan kasuwar Ghana a Burkina Faso ya sa farashin tumatur ya tashi
Naɗin 'ya'yan Dangote mata uku a manyan muƙamai: Sabon babi a tsarin gado na kasuwancin iyali
China za ta soke karɓar harajin fitar da kayayyaki daga ƙasashen Afirka 53
Me ya sa farashin zinare ke tashi a lokacin rikicin siyasa a duniya?
Gwamnatocin Afirka sun juya ga tsarin Bankin Musulunci bayan nasarar Sukuk a Benin
Ana sa ran kasuwanci tsakanin Turkiyya da Nijeriya ya kai dala biliyan 10 saboda sabbin yarjeniyoyi
Afrika na amfani da tagomashin da zinari yake samu don ƙara ƙarfin arziƙinta
Ghana ta biya basussukan dala biliyan 1.47 na fannin makashi da ake bin ta
Trump ya ce Amurka za ta karɓi gangar ɗanyen mai miliyan 50 daga Venezuela
Kamfanin Dangote ya yi watsi da ikirarin rufe matatar mansa
Me ya sa hanyoyin teku da aka toshe ke tayar da kura a Gabashin Afirka?
ECOWAS za ta cire harajin tafiye-tafiyen jiragen sama tsakanin ƙasashen Yammacin Afrika a 2026
Manyan ƙere-ƙeren fasaha na Afirka da suka yi tasiri a duniya
Abu biyar da ya kamata ku sani kan Taron G20 na farko a Afirka
An cire Nijeriya daga jerin kasashen da ake sa wa ido kan safarar kudade ba bisa ka'ida ba a duniya
Bai kamata kasuwanci da Afirka ya zama buƙatar ɗiban ma’adanai ba: Ministan Nijeriya Tuggar
Jamhuriyar Nijar ta kafa cibiyar tsaron intanet
Kamfanin simintin Dangote ya fara aiki a ƙasar Ivory Coast