Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF a Kudancin Kordofan
Da yake magana da Anadolu a ranar Laraba, majiyoyin sun ce rundunonin soji sun yi fito na fito da harin tun da wuri a safiyar, wanda ya yi nufin jawo asarar rayuka da kayan aiki kuma suka tilasta wa maharan janyewa.
Sojojin Sudan sun daƙile wani babban hari da ‘yan tawayen (RSF) da abokiyarta, Sudan People’s Liberation Movement–North (SLPM-N), suka kai wa garin Al-Kuweik a Kudancin Kordofan, in ji majiyoyin soji.
Da yake magana da Anadolu a ranar Laraba, majiyoyin sun ce rundunonin soji sun yi fito na fito da harin tun da wuri a safiyar, wanda ya yi nufin jawo asarar rayuka da kayan aiki kuma suka tilasta wa maharan janyewa.
Sun kara da cewa dakarun gwamnati sun kwace motoci masu sulke da na yaki a lokacin fafatawar.
Babu wani martani nan take daga RSF ko SPLM-North kan rahoton.
Bidiyoyi da sojoji suka yada a kafafen sada zumunta sun nuna murnar da aka dinga yi bayan an daƙile harin.
A 'yan makonnin da suka gabata, jihohin Kordofan guda uku na Sudan — Arewa, Yamma da Kudu — sun sha fama da munanan rikice-rikice tsakanin sojoji da RSF, wanda ya tilasta dubban fararen hula barin gidajensu.
Daga cikin jihohin Sudan 18, RSF na da iko da dukkan jihohi biyar na yankin Darfur a yamma, sai dai wasu sassan arewacin North Darfur da ke ci gaba da kasancewa karkashin ikon sojoji.
A gefe guda, sojoji suna rike da mafi yawan wurare na sauran jihohi 13 a kudu, arewa, gabas da tsakiyar kasar, ciki har da babban birnin Khartoum.
Rikicin tsakanin sojojin Sudan da RSF, wanda ya fara a watan Afrilu 2023, ya yi sanadin kashe dubban mutane kuma ya tilasta miliyoyin mutane barin gidajensu.